Friday, June 26
Shadow

Bazan taba bayar da kudi dan yiwa mutane auren gata a mazabata ba saboda bana son ganin karin yara da yawa>>Inji Dan majalisar Tarayya, Bello El-Rufai

Dan majalisar wakilai ta tarayya kuma da a wajan tsohon gwamnan jihar Kaduna, Bello El-Rufai ya bayyana cewa ba zai taba biyan kudi a yiwa mutane auren gata a mazabarsa ba.

Ya bayyana hakane a wata hira da aka yo dashi wadda hutudole ya bibiya.

Yace dalilinsa kuwa baya son ganin karin yawan yara.

Yace a yanzu haka a Arewa yawanmu ya wuce kima amma kuma bamu da isashshen ilimi.

https://twitter.com/IU_Wakilii/status/1852740532964855995?t=ZXKaUEF7mQX2zUghhpdiIg&s=19

Lamarin yawa da almajirci na kananan yara dai a bayyane yake a Arewacin Najeriya.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyon: Duk da wajan Taron Rainbow yacewa jam'iyyar ADC ya fasa basu dakin taron da zasu yi babban taronsu saboda Wike ya hanasu, Jam'iyyar ta ADC tace babu gudu ba ja da baya sai sun yi taronsu a wajan saidai duk abinda zai faru ya faru

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *