Friday, March 13
Shadow

Duk Labarai

Kalli Bidiyon: Matashin nan na Kano da ya fito ya nuna bacin ransa bayan ya kai Mahaifiyarsa Asibiti amma babu gado ya fito ya baiwa Gwamnan Kano Hakuri

Kalli Bidiyon: Matashin nan na Kano da ya fito ya nuna bacin ransa bayan ya kai Mahaifiyarsa Asibiti amma babu gado ya fito ya baiwa Gwamnan Kano Hakuri

Duk Labarai
Matashi na jihar Kano da ya nuna bacin ransa bayan da ya kai mahaifiyarsa Asibiti a Kanon amma ya iske ba Gado ya fito ya bayar da Hakuri. Matashin yace shi ba dan siyasa bane kuma yana baiwa gwamnan Kano Hakuri kuma bai yi dan ya zagi kowa ba. Yace duk ma wanda ya ji Haushi saboda maganar tasa yana bashi Hakuri. https://www.tiktok.com/@aliban80/video/7587158910537125128?_t=ZS-92UA4wnp3Nw&_r=1
Kalli Bidiyon: Yanda Tankar Dakon man fetur ta yi ta ho mu gama da tawagar motocin kakakin majalisar Dattijai Godswill Akpabio

Kalli Bidiyon: Yanda Tankar Dakon man fetur ta yi ta ho mu gama da tawagar motocin kakakin majalisar Dattijai Godswill Akpabio

Duk Labarai
Kakakin Majalisar Dattijai, Godswill Akpabio ya bayyana cewa tankar dakon man fetur ta yi taho mu gama da daya daga cikin motocin dake tawagarsa. Lamarin ya farune a Ibadan jihar Oyo ranar Lahadi, kamar yanda Akpabio ya sanar a zaman majalisar. Yace daya daga cikin 'yansandan dake masa rakiya, Ibrahim Hussain ya rigamu gidan gaskiya kuma har an binneshi. https://twitter.com/Onsogbu/status/2003590433721798994?t=qqOwu52roVLBzeGd6Ll2GQ&s=19
Kalli Bidiyon: Malamin Addinin Islama, Bayerabe, Ahlussunah yace Bikin Eyo Festival na Al’adun Yarbawa da shugaba Tinubu ya halarta shirkane

Kalli Bidiyon: Malamin Addinin Islama, Bayerabe, Ahlussunah yace Bikin Eyo Festival na Al’adun Yarbawa da shugaba Tinubu ya halarta shirkane

Duk Labarai
Wani malamin addinin Islama Bayerabe, Ahlussunah me suna Shaykh AbdulHakīm AbdurRaheem Al Kutubi ya bayyana cewa Bikin Eyo Festival na al'adun Yarbawa da shugaba Tinubu da matarsa Remi suka halarta shirkane. Malamin yace musulmi bai kamata ya halacci wannan bikin ba. https://twitter.com/muslimsconnect0/status/2003552885582496245?t=D6G9iUxD3vBN12lu-rFBNg&s=19 Shugaba Tinubu bayan ya je Legas inda yake hutun Kirsimeti acan an ganshi a wajan Bikin Eyo Festival inda aka ganshi suna rawa shi da matarsa Remi. Hutudole ya fahimci cewa, wannan bikin ana yinshi ne dan girmama wasu manyan mutane a kabilar yarbawa da suka mutu wanda har bauta musu ana yi, da kuma girmama masu sarautun gargajiya.
Kalli Bidiyon: Ganin Kakakin majalisar Dattijai, Sanata Godswill Akpabio yana tafiya da kyar ya dauki hankula

Kalli Bidiyon: Ganin Kakakin majalisar Dattijai, Sanata Godswill Akpabio yana tafiya da kyar ya dauki hankula

Duk Labarai
An ga Bidiyon kakakin majalisar Dattijai, Sanata Godswill Akpabio na tafiya da kyar. Bidiyon an daukeshi ne yayin da Akpabio ya je wajan nadin sarautar da akawa dan shugaban kasa, Seyi Tinubu. https://twitter.com/RealQueenBee__/status/2003508528309502101?t=nAasLDy3dRVii8QbDnNzeA&s=19 A baya dai Sahara reporters ta ruwaito cewa, Godswill Akpabio ya yanke jiki ya fadi an fita dashi zuwa kasar Ingila, amma ya musanta hakan.
Kalli Bidiyon:Matashi ya dauki Hankula bayan da ya kai mahaifiyarsa Asibiti a Kano amma akace ba gado

Kalli Bidiyon:Matashi ya dauki Hankula bayan da ya kai mahaifiyarsa Asibiti a Kano amma akace ba gado

Duk Labarai
Wannan matashin ya dauki hankula sosai bayan da ya kai mahaifiyarsa Asibiti a Kano aka ce ba gado. Matashin ya yi Bidiyo yanawa shuwagabanni Allah ya isa. Yace ba zai taba yafe hakkinsa dake kan shuwagabannin da suka ki daukar matakin da ya dace ba. https://twitter.com/malantrent/status/2003429579789337044?t=2NNsS09z3FffM54q68Jr7Q&s=19 j
Da Duminsa: Gwamnati na shirin kama Atiku Abubakar, Sheikh Isa Ali Pantami da Nasiru Ahmad El-Rufai

Da Duminsa: Gwamnati na shirin kama Atiku Abubakar, Sheikh Isa Ali Pantami da Nasiru Ahmad El-Rufai

Duk Labarai
Wani me sharhi akan al'amuran yau da kullun, Adekunle Adebayo, ya kwarmata cewa Gwamnati na shirin kama tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar. Hakanan tana son kama Tsohon Ministan sufuri, Rotimi Amaechi da Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai. Adekunle Adebayo ya bayyana hakane a wata sanarwa da ya aikewa jaridar DailyPost ya bayyana cewa wannan shirine na dakile 'yan Adawa da samar da jam'iyyar siyasa kwaya daya tilo a Najeriya. Sauran wadanda ya ce za'a kama sun hada da Isa Ali Pantami, Rauf Aregbesola, Kashim Ibrahim Imam. Saidai yace idan aka yi wannan kamen ya sabawa dokar kasa.
Saidu Mohammed ya karbi shugabancin hukumar NMDPRA daga hannun Farouk Ahmed

Saidu Mohammed ya karbi shugabancin hukumar NMDPRA daga hannun Farouk Ahmed

Duk Labarai
Saidu Mohammed ya karbi shugabancin hukumar NMDPRA daga hannun Farouk Ahmed. Farouk Ahmed dai shine shugaban Hukumar NMDPRA wanda Attajirin Najeriya, Aliko Dangote yawa tonon Silili yace ya biyawa 'ya'yansa kudin makaranta har dala Miliyan 7 a kasar Switzerland. Dangote dai ya kai Farouk kara hukumar ICPC inda ya nemi a bincikeshi. Daga karshe Farouk ya ajiye mukaminsa. Hukumar NMDPRA tace wannan canjin shugabancin da aka samu zai tabbatar da ci gaba da kuma yin aiki yanda ya kamata.