Tuesday, March 17
Shadow

Duk Labarai

Kalli Bidiyon: Ni dai Billahillazi ko nawa za’a biyani ba zan iya aikin soja ba, saboda banso a Shyekye ni a irin wannan hanyar>>Inji Sanata Ali Ndume

Kalli Bidiyon: Ni dai Billahillazi ko nawa za’a biyani ba zan iya aikin soja ba, saboda banso a Shyekye ni a irin wannan hanyar>>Inji Sanata Ali Ndume

Duk Labarai
Sanata Ali Ndume daga jihar Borno ya bayyana cewa, shi ko nawa za'a biyashi ba zai iya aikin soja ba. Yace dalili kuwa shine ba ya son ya mutu a irin wannan hayar ba saboda ko ya mutu babu wanda zai san darajarsa. Ya bayar da misalin cewa, yanzu ga gawar Janar can watau(Brigadier Mohammed Uba) a daji har yanzu ba'a dawo da ita ba. https://twitter.com/channelstv/status/1994113706431496508?t=qyEyfHxF69l_yfczxx6Now&s=19
Maganar janye ‘Yansanda daga baiwa manyan mutane tsaro ba gudu ba ja da baya, Babu wanu Gwamna ki Minista da zan saurara saboda umarnin shugaban kasa ne>>Inji IGP Kayode Egbetokun

Maganar janye ‘Yansanda daga baiwa manyan mutane tsaro ba gudu ba ja da baya, Babu wanu Gwamna ki Minista da zan saurara saboda umarnin shugaban kasa ne>>Inji IGP Kayode Egbetokun

Duk Labarai
Shugaban 'yansandan Najeriya, Kayode Egbetokun ya bayyana cewa maganar janye 'yansanda daga baiwa manyan mutane tsaro abune wanda ba gudu ba ja da baya. Ya bayyana hakane a wata ganawa da manema labarai da yayi. Yace dama can suna haka amma tunda yanzu Umarni ya zo daga wajan shugaban kasa, babu wani Minista ko Gwamna da zai kirashi da sunan neman Alfarma. Yace ya ga ana ta yada wani labari wai akwai 'yansanda 130,000 dake baiwa manyan mutane tsaro a fadin Najeriya, yace ba gaskiya bane hakan. https://twitter.com/ChuksEricE/status/1994070671362503142?t=bnMol8AgIrTz6aIacQM8YA&s=19
Ba Daidai bane ace an yankewa Nnamdy Khanu hukuncin daurin rai da rai ba amma wasu masu laifi irin nasa an yanke musu hukuncin daurin shekaru 20 ba>>Inji Bello El-Rufai

Ba Daidai bane ace an yankewa Nnamdy Khanu hukuncin daurin rai da rai ba amma wasu masu laifi irin nasa an yanke musu hukuncin daurin shekaru 20 ba>>Inji Bello El-Rufai

Duk Labarai
Dan majalisar Wakilai daga jihar Kaduna, Bello El-Rufai ya bayyana rashin dacewar yankewa Nnamdy Khanu hukuncin daurin rai da rai amma kuma aka yankewa wasu a ake zargi da aikata tà'àddànci hukuncin daurin shakeru 20. Ya bayyana hakane a zaman Majalisar inda yake kawo muhimmancin samar da tsaro mazabu. https://twitter.com/ChuksEricE/status/1994119629862826242?t=rF4RLikI_Qn5E0GffBNhyg&s=19
Kalli Bidiyon: Ina Kira Ga ‘yan Izala da su fito su nesanta kansu da masu fadar kalaman da basu dace ba akan rasuwar Sheikh Dahiru Usman Bauchi >>Inji Digital Imam

Kalli Bidiyon: Ina Kira Ga ‘yan Izala da su fito su nesanta kansu da masu fadar kalaman da basu dace ba akan rasuwar Sheikh Dahiru Usman Bauchi >>Inji Digital Imam

Duk Labarai
Malamin Addinin Islama, Digital Imam ya bayyana cewa, yana kira ga malaman Izala da su fito su barranta da masu fadar kalaman sa basu dace ba akan Rasuwar Sheikh Dahiru Usman Bauchi. Yace yin Shiru kamar yadda da abinda masu zagin ke yi ne. https://www.tiktok.com/@digital_imaam/video/7577495912365182229?_t=ZS-91lD6xeBYum&_r=1
Kalli Bidiyon: Shin wai ina Kunyar mu take ne? Ji yanda mata kewa halittar Bilal Villa ba’a bayan ganinsa da gajeren wando

Kalli Bidiyon: Shin wai ina Kunyar mu take ne? Ji yanda mata kewa halittar Bilal Villa ba’a bayan ganinsa da gajeren wando

Duk Labarai
Matashin Mawakin Arewa, Bilal Villa ya wallafa wani Bidiyo inda aka ganshi sanye da gajeren Wando. A Bidiyon an ga yana saka kaya da daya-daya har ya kammala saka kayan gaba daya. Lamarin ya dauki hankula sosai inda musamman mata suka rikawa Al'aurarsa ba'a. Wata tace ta ganta kamar ta yara wata kuma tace ta ganta kamar Charbin malam da sauransu. https://www.tiktok.com/@bilalvillah/video/7576449008571387147?_t=ZS-91l92aI3L96&_r=1
Sheikh Ɗahiru Bauchi dattijo ne mai son zaman lafiya – Kwankwanso

Sheikh Ɗahiru Bauchi dattijo ne mai son zaman lafiya – Kwankwanso

Duk Labarai
Tshon ɗan takarar shugaban Najeriya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya bayyana jimaminsa tare a miƙa ta'aziyya ga iyalai da ƴanuwan da makusantan Sheikh Ɗahiru Usman Bauchi bisa rasuwar malamin. Kwankwaso ya bayyana malamin a matsayin uba, kuma babban malami wanda koyarsa ta zama madubi ga ɗimbin al'umma. "Ta hanyar karantarwa, Sheikh Ɗahiru taɓa rayuwar al'umma da dama tare da jan hankalinsu wajen koyi da halaye masu kyau da kuma ƙaunar Alqur'ani da sunnar manzon Allah." Kwankwaso ya ce shehin mutum ne mai son zaman lafiya kuma dattijo mai ƙoƙarin haɗa kan ƴan ƙasa, "wanda kuma ba za mu manta da shi ba, kuma ƙasarmu ba za ta manta da shi." "A madadin iyalina da ni kaina, ina miƙa ta'aziya da iyalansa da ɗalibansa da gwamnati da al'ummar Bauchi bisa wannan rasuwa. Allah ya saka sh...
Duk Da rokon da ‘yan majalisar Tarayya suka wa shugaba Tinubu kar a janye, Hukumar ‘yansandan Najeriya ta janye ‘yansanda dubu sha daya masu Baiwa manyan mutane kariya a Najeriya

Duk Da rokon da ‘yan majalisar Tarayya suka wa shugaba Tinubu kar a janye, Hukumar ‘yansandan Najeriya ta janye ‘yansanda dubu sha daya masu Baiwa manyan mutane kariya a Najeriya

Duk Labarai
Sufeto Janar na 'Yansandan Najeriya Olukayode Egbetokun ya ce sun aiwatar da umarnin Shugaban Ƙasa Bola Tinubu na janye dakarunsu daga gadin ɗaiɗaikun mutane da ake kira VIP. Yayin wani taron manema labarai a yau Alhamis, IG Egbetokun ya ce zuwa yanzu sun janye dakaru 11,566 daga gadin manyan mutane a faɗin Najeriya. "Wannan karon za muj aiwatar da umarnin da kyau saboda umarnin shugaban ƙasa ne," in ji shi. "Babu wani gwamna, ko minista, ko abokaina da za su kira su takura min saboda sun san cewa umarnin shugaban ƙasa ne. Ina da tabbacin ba za su uzura wa kwamashinonin 'yansanda ba ma." Ya ƙara da cewa za su tura jami'an da aka janye zuwa "wuraren da aka fi buƙatarsu, musamman a wannan lokaci mai muhimmanci".
Shugaba Tinubu ya yi Allawadai ta juyin mulkin Guinea-Bissau

Shugaba Tinubu ya yi Allawadai ta juyin mulkin Guinea-Bissau

Duk Labarai
Gwamnatin Najeriya ta yi Allah Wadai da juyin Mulkin da aka yi a Guinea-Bissau, inda ta buƙaci a dawo da mulkin dimokraɗiyya a ƙasar. A cikin wata sanarwa da ma'aikatar kula da harkokin ƙasashen waje na ƙasar ta fitar a yau alhamis, Najeriya ta ce ta damu matuƙa game da lamarin, inda ta bayyana ƙwace mulkin a matsayin 'abin takaici' '' Juyin mulkin na bayyana karya dokokin ECOWAS na mulkin dimokraɗiyya da gwamnati mai adalci, waɗanda suka haramta hawa mulki ta hanyar da ba na tsarin mulki ba.'' inji sanarwar. Ma'aikatar harkokin wajen ta kuma ce Najeriya na tare da ƴan ƙasar Guinea Bissau, kuma ta na kiran dawo wa mulkin dimokradiyyar, da dawo da dukkanin waɗanda ake riƙe da su.