Friday, February 27
Shadow

Duk Labarai

Da Duminsa: Kungiyar Malaman Jami’a ta ASUU ta tsunduma yajin aikin gargadi na sati biyu

Da Duminsa: Kungiyar Malaman Jami’a ta ASUU ta tsunduma yajin aikin gargadi na sati biyu

Duk Labarai
Ƙungiyar malaman jami'a a Najeriya Asuu ta bai wa mambobinta umarnin fara yajin aiki daga gobe Litinin na tsawon mako biyu. Academic Staff Union of Universities (Asuu) ta ce yajin aikin na gargaɗi ne bayan cikar wa'adin da suka bai wa gwamnatin Najeriya a watan Satumban da ya gabata. Shugaban Asuu Farfesa Chris Piwuna ya faɗa yayin taron manema labarai a Abuja cewa matakin ya zama dole "saboda gazawar gwamnatin wajen biyan buƙatunmu".
Da Duminsa: Tinubu zai tafi Italiya yau Lahadi

Da Duminsa: Tinubu zai tafi Italiya yau Lahadi

Duk Labarai
Shugaban Najeriya Bola Tnubu zai kama hanyar zuwa Italiya a yau Lahadi domin halartar taron Aqaba na shugabannin ƙasashe kan tsaro. Fadar shugaban ƙasar ta ce taron Aqaba Process Heads of State and Government Level Meeting zai mayar da hankali kan matsalar tsaro a Afirka ta Yamma. "Za a fara taron ranar 14 ga watan Oktoba, wanda zai haɗa shugabannin ƙasa, da shugabannin soji daga Afirka domin tattauna ƙalubalen tsaro a Afirka ta Yamma," in ji sanarwar da fadar ta fitar ranar Asabar da dare. Sarkin Jordan Abdullah II ne ya ƙaddamar da taron a 2015 domin yaƙi da ta'addanci, wanda Masarautar Jordan da gwamnatin Italiya ke gudanarwa, a cewar sanarwar. "Shugaba Tinubu zai tattauna da wasu shugabanni a gefen taron domin lalubo hanyoyin magance matsalar tsaro a yankin," kamar yadda fa...
A shirye nake in auri Maryam Sanda bayan da shugaba Tinubu ya mata Afuwa>>Inji Matashi, Sarki

A shirye nake in auri Maryam Sanda bayan da shugaba Tinubu ya mata Afuwa>>Inji Matashi, Sarki

Duk Labarai
Matashi me amfani da sunan Sarki a X ya bayyana cewa, a shirye yake ya auri Maryam Sanda a matsayin mace ta biyu. Ya bayyana hakane bayan da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya mata afuwa. Maryam Sanda dai ta kashe mijinta ne wanda dalilin haka kotu ta yanke mata hukuncin kisa. Saidai a cikin jerin wadanda shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya wa Afuwa an ga sunan Maryam Sanda. Wasu dai sun alakanta wannan afuwa da cewa kudi ne suka sa aka mata inda wasu ke cewa, Hanya ce.
Kalli Bidiyon: Mafi yawancin matan aure yanzu duk Qaruwaine, kuma suna shaye-shaye, saidai ni na yi sa’a ban taba kama matata da Qwarto ba>>Inji Gfresh

Kalli Bidiyon: Mafi yawancin matan aure yanzu duk Qaruwaine, kuma suna shaye-shaye, saidai ni na yi sa’a ban taba kama matata da Qwarto ba>>Inji Gfresh

Duk Labarai
Tauraron Tiktok, Gfresh Al-amin ya bayyana cewa a duk cikin matan da ya aura babu wadda yafi jin dadin zama da ita da nutsuwa kamar ta yanzu, 'yar Yola. Gfresh yace Mafi yawancin matan aure yanzu Qaruwaine, aure baya hanasu neman maza. hakanaan yace kuma suna shaye-shayen miyagun Kwayoyi. https://www.tiktok.com/@gfreshfanpage/video/7560075106840546568?_t=ZS-90U32qmFGNs&_r=1
Kalli Bidiyon: Ban ce Ahlussunah basa son Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) ba, cewa nayi ‘yan Dariqa sun fi Ahlussunah na yanzu son Annabi, kuma ina nan akan bakana>>Inji Sheikh Nura Khalid

Kalli Bidiyon: Ban ce Ahlussunah basa son Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) ba, cewa nayi ‘yan Dariqa sun fi Ahlussunah na yanzu son Annabi, kuma ina nan akan bakana>>Inji Sheikh Nura Khalid

Duk Labarai
Malamin Addinin Islama, Sheikh Nura Khalid, Wanda aka fi sani da Digital Imam ya bayyana cewa, bai ce 'yan Izala basa son Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) ba. Abinda ya fada shine 'yan Darika sun fi son Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam). Yace dalilinsa kuwa shine su sufaye sun ce duk Hadisin da ya kawo aibu ga Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) basa neman ingancinsa ko rashin ingancinsa, basu yadda dashi bane. Hakanan duk Hadisin da ya kawo Yabo ga Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) suna yadda dashi ba tare da neman inganci ko rashin inganci ba. Yace su kuma Ahlussunah na yanzu suna neman Hadisai da suka aibata Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) ne suna karantar da mutane. Malam yace to a tsakaninsu waye yafi son Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam)? https://www.tiktok....
Kalli Bidiyon: Tunda kake ta taba jina ina kare kainda dan an zageni? Ni ina fitowa in yi martanine idan an taba addini>>Inji Malam Aminu Ibrahim Daurawa

Kalli Bidiyon: Tunda kake ta taba jina ina kare kainda dan an zageni? Ni ina fitowa in yi martanine idan an taba addini>>Inji Malam Aminu Ibrahim Daurawa

Duk Labarai
Babban malamin Addinin Islama, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ya bayyana cewa, dan an zageshi baya fitowa ya kare kanshi. Ya bayyana hakane a wani Bidiyo da ya wallafa inda yace shi sai idan an taba addini ne yake fitowa yayi martani. Malam Daurawa yace tarbiyyar da malaminsu ya koyar dasu kenan inda yace su baiwa addini Kariya su kuma Allah zai basu kariya. https://vt.tiktok.com/ZSUDF8FQy
An kori wata malamar coci daga cocin saboda tace ta musulunta, saidai tace karyane, ba dalilin kenan ba, An nemi a mayar da ita Qaruwar cocinne, ana nemanta da lalata taki yadda shiyasa suka koreta

An kori wata malamar coci daga cocin saboda tace ta musulunta, saidai tace karyane, ba dalilin kenan ba, An nemi a mayar da ita Qaruwar cocinne, ana nemanta da lalata taki yadda shiyasa suka koreta

Duk Labarai
Wata malamar coci me suna Annastasia Kinse wadda 'yar Asalin jihar Filato ce dake a matsayin malamar cocin Katolika dake jihar Edo tace an koreta daga aiki ne saboda ta ki yadda ta zama karuwa a cocin kowa ya rika nemanta. Ta bayyana hakane a hirar da aka yi da ita a jaridar Punchng. Kinse itace reverend sister ta farko a kauyensu kuma tana aiki da jami'ar Veritas University sannan tana karatun digiri na biyu, watau Masters a jami'ar Abuja kamin a koreta daga aiki. Tace a shekarar 2015 ne ta shiga aikin cocin kuma ta y aiki da cocin na tsawon shekarau 2 kamin ta samu kwarewa. Tace a watan July na shekarar 2025 ne aka fitar da takardar cewa an koreta daga cocin saboda ta koma musulma, amma ace karyane saboda ta kai karar nemanta da lalata da aka yi n yasa aka koreta. Tace t...
Kalli Bidiyo: Masu kudi na Allah da Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) basu wuce mutane 20 ba a Najeriya, Sauran duk barayine>>Inji Ordinary President

Kalli Bidiyo: Masu kudi na Allah da Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) basu wuce mutane 20 ba a Najeriya, Sauran duk barayine>>Inji Ordinary President

Duk Labarai
Ahmad Isa, Ordinary President ya bayyana cewa, a Najeriya masu kudi na Allah da Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) basu wuce mutane 20 ba. Yace sauran duk Barayine. Ya bayyana cewa, yasan zai yi bakin jini amma zai fada saboda yasan gaskiya idan bai fada ba ya taimakawa zalinci. https://www.tiktok.com/@3star.jr/video/7556671494181391672?_t=ZS-90StGdJRFOC&_r=1
Masu wakokin Yabon Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) Sufayene, Kuma wallahi sunfi son Annabi, amma kun dage sai kun gano Laifinsu>>Sheikh Nura Khalid, Digital Imam

Masu wakokin Yabon Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) Sufayene, Kuma wallahi sunfi son Annabi, amma kun dage sai kun gano Laifinsu>>Sheikh Nura Khalid, Digital Imam

Duk Labarai
Malamin addinin Islama, Sheikh Nura Khalid ya bayyana cewa, Sufayene ke wakokin yabon Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam). Yace amma wanda basa yi sun sasu gaba sai sun gano inda suke kuskure. Yace duk wanda ya dauki littafin wani yana neman kuskure to zai ga kuskuren, saidai ya nemi a shafawa masu yabon Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) Lafiya. https://www.tiktok.com/@shaaweuei5p/video/7559703374237584658?_t=ZS-90TqKDQcfVQ&_r=1
EFCC ta kama Mamud Nasidi da Yahaya Nasidi a filin jirgin sama na legas da zunzurutun kudade har dala $6,180 da da fan £53,415

EFCC ta kama Mamud Nasidi da Yahaya Nasidi a filin jirgin sama na legas da zunzurutun kudade har dala $6,180 da da fan £53,415

Duk Labarai
Hukumar yaki da rashawa da cin hanci, EFCC ta kama Mamud Nasidi da Yahaya Nasidi, bisa kin bayyana makudan kudaden da suke dauke dasu da suka kai dala $6,180 da da fan £53,415 a filin jirgin sama na Legas. Jami'an kula da filin jirgin saman, (FAAN) ne suka kama masu laifin inda suka damkasu hannun EFCC. Tuni EFCC ta sanar da cewa ta fea bincike kan wadanda ake zargin. Wadanda ake zargin sun zo ne daga Dubai inda suke shirin wucewa zuwa Abuja. An kuma kwace wayoyi guda 3 daga hannunsu.