Friday, February 27
Shadow

Duk Labarai

Darajar naira na farfaɗowa

Darajar naira na farfaɗowa

Duk Labarai
Farashin dalar Amurka na ci gaba da sauka a Najeriya, inda a wasu kasuwannin bayan fage ake sayar da dalar daya a kusan naira 1,450. Wannan farashi ya yi kasa idan aka kwatanta da na makonnin baya, inda darajar dala ta kai har naira 1,560 a wasu wuraren. A jihar Kano, cibiyar harkokin kasuwancin arewacin Najeriya, masu hada-hadar kudaden kasashen ketare sun tabbatar da cewa farashin dalar na ta sauka a kullum. Shugaban ƙungiyar masu canjin kuɗaɗen waje a jihar, Alhaji Sani Salisu Dada, ya ce, "Dangane da faduwar darajar dala, kusan sati biyu kenan a kowace rana tana karyewa. Idan aka duba baya, dalar ta kai kusan naira 1,560, amma a yau Babban Bankin ƙasa yana sayarwa a kan naira 1,466, yayin da kasuwar bayan fage take a naira 1,450." "A halin yanzu farashinmu ya fi armashi, sa...
Kalli Bidiyo: Awara nake toyawa a kofar Gidanmu amma naga wata kawata na saka kaya masu tsada shiyasa na shiga Harkar Fim>>Inji A’isha Najamu

Kalli Bidiyo: Awara nake toyawa a kofar Gidanmu amma naga wata kawata na saka kaya masu tsada shiyasa na shiga Harkar Fim>>Inji A’isha Najamu

Duk Labarai
Tauraruwar fina-finan Hausa, A'isha Najamu ta bayyana cewa daga jihar Jigawa take, Garki Gari. Sannan tace Wara take toyawa a kofar Gidansu amma daga baya ta fara ganin kawarta da kaya masu tsada, shiyasa itama ta shiga fim. Ta bayyana hakane a wata hira da aka yi da ita. Kalli Bidiyon hirar anan: https://www.tiktok.com/@abdooltilde40/video/7556371413788118280?_t=ZS-90FfDaVTV57&_r=1
Na Gano cewa: Yawanci mazan Kano basa iya ciyar da matansu, sannan ana yiwa yara mata auren wuri>>Inji Sarkin Kano, Muhammad Sanusi II

Na Gano cewa: Yawanci mazan Kano basa iya ciyar da matansu, sannan ana yiwa yara mata auren wuri>>Inji Sarkin Kano, Muhammad Sanusi II

Duk Labarai
Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II ya ce dole ne a gyara zamantakewar aure a tsakanin ma'auarata a jihar Kano kasancewar matsalar ce ta fi damun al'ummar jihar Kano. Sarkin na Kano ya ce ƙararrakin ciyarwa su ne kaso mafi yawa na shari'o'in aure da aka fi samu cikin kotunan jihar a shekarun baya-bayan nan. Wannan wani ɓangare ne na kundin binciken digiri na uku na dokar shari'ar Musulunci da Khalifa Muhammadu Sanusi ya rubuta bayan kammala karatunsa a Jami'ar London. Auren kananan yara Sarki Muhammadu Sanusi ya ce wani abun da ya fahimta shi ne idan ana son a kawo ƙarshen yi wa ƙananan yara aure dole ne sai gwamnati ta taka muhimmiyar rawa. "Har yanzu ina kan ra'ayin lallai ya kamata a bar yarinya sai ta girma a yi mata aure. Kuma a cikin bincike abubuwa da dama sun bayy...
Tinubu dan kasuwane, Tara Dukiya yazo yi kamar sauran shuwagabannin Najeriya >>Inji Fasto Odumeje

Tinubu dan kasuwane, Tara Dukiya yazo yi kamar sauran shuwagabannin Najeriya >>Inji Fasto Odumeje

Duk Labarai
Fasto Odumeje ya bayyana shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a matsayin dan kasuwa wanda ya zo tarawa kansa sa iyalinsa dukiya. Odumeje ya bayyana cewa shuwagabanni sune irin su Ibrahim Traore da Xi jingping na China da sauransu. Yace amma mafi yawancin 'yan siyasar Najeriya tara abin Duniya ne a gabansu. https://www.youtube.com/watch?v=CY4KYfiCz4k?si=ZDouMlQ6dZDXKPCa
Dangote ya nace akan shi fa ba zai mayar da ma’aikata ‘yan Najeriya 800 daya kora aiki daga matatar mansa ba saboda bai yadda dasu ba, zasu iya yi masa zagon kasa

Dangote ya nace akan shi fa ba zai mayar da ma’aikata ‘yan Najeriya 800 daya kora aiki daga matatar mansa ba saboda bai yadda dasu ba, zasu iya yi masa zagon kasa

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana kan dalilin da yasa Dangote ya kori ma'ikatan Najeriya 800 daga aiki sannan dalilin da yasa ya ki mayar dasu aiki. Dangote yace ya samesu da yi masa zagon kasa ne wanda hakan ya shafi yanayin matatar. Saidai korar ma'aikatan ya tilasta kungiyar manyan ma'aikatan man fetur da Gas, PENGASSAN shiga yajin aiki dan Dangoten ya mayar da wadancan ma'ikata da ya sallama daga aiki. Saidai Dangote yace shi fa ba zai mayar da ma'ikatan da bai yadda dasu ba bakin aiki, dalili kuwa shine zasu yi masa zagon kasa. Dangote yace zai biya ma'aikatan albashi har na tsawon shakeru biyu ba tare da suna zuwa aiki ba, saidai Gwamnatin tarayya ta ja hankalinsa kan yawan kudin da zai kashe idan yace zai yi hakan. Amma Dangote yace ya amince yayi asarar biyansu kudin Albashi ba ...
Kalli Hoto Yanda Likitoci suka cire Chokula 29 da Burosh din wanke baki guda 19 daga cikin wani mutum

Kalli Hoto Yanda Likitoci suka cire Chokula 29 da Burosh din wanke baki guda 19 daga cikin wani mutum

Duk Labarai
Likitoci a asibitin Devnandani Hospital, Hapur, dake kasar India sun ciro abubuwa 50 da wani mutum dan shekaru 40 ya hadiya daga cikinsa. Likitocin sun kwashe awanni 5 suna wannan aiki, kamar yanda rahotanni suka bayyana. Ranar 17 ga watan Satumba aka kaishi asibiti yana aman jini inda aka mai Scanning aka ga Cokulan karfe 29 da burosh 19 da kuma biro guda 2. Lamarin ya baiwa likitocin mamaki. Shugaban Likitocin da suka yi wannan aiki, Dr. Shyam Kumar ya bayyana cewa, bai taba ganin irin wannan abubuwan a cikin mutum daya ba. Ya kara da cewa an babballa abubuwan kamin mutumin ya hadiyesu. Mutumin ya aikata hakanne bayan da aka kaishi wani gidan horo da baya so. Rahoton yace yana samun sauki bayan da aka masa aiki.