
Wahalar rayuwa tasa yanzu matasan Najeriya na zuwa kasar Nijar neman aiki>>Jafar Jafar
Shahararren dan jarida, Jafar Jafar ya bayyana cewa a shekarun baya, matasa daga kasar Nijar na zuwa Najeriya dan yin aikin gadi da tura ruwa da sauransu.
Yace amma yanzu labari ya canja inda, musamman saboda faduwar darajar Naira, matasan Najeriya sai shiga kasar Nijar suke neman aikin yi.