Monday, March 2
Shadow

Duk Labarai

Da Duminsa: Hukumar kula da jiragen kasa ta Najeriya, NRC, ta dakatar da jigilar fasinja daga Kaduna zuwa Abuja

Da Duminsa: Hukumar kula da jiragen kasa ta Najeriya, NRC, ta dakatar da jigilar fasinja daga Kaduna zuwa Abuja

Duk Labarai
Hukumar kula da sufurin jiragen kasa ta Najeriya, NRC ta sanar da dakatar da sufurin jirgin kasa daga Abuja zuwa Kaduna, har sai abinda hali yayi. Hukumar ta sanar da hakane jim kadan bayan hadarin da aka samu bayan tashin jirgin kasan daga Abuja zuwa Kaduna bayan da ya kaucewa taragonsa. Daraktan hukumar, Kayode Opeifa ne ya sanar da haka a Abuja ga manema labarai, Ya musanta rade-radin da ake yi cewa dama jirgin kasan yana da matsala. Yace jami'an hukumar su dana hukumar bincike ta kasa, (NSIB) sun halarci wajan faruwar hadarin inda yace suna kan bincike kan lamarin. Ya kuma kara da cewa, sun fara shirin mayarwa da fasinjojin fake cikin jirgin kudaden tikiti da suka saya. Yace mutane 6 sun ji raunika ba masu muni ba kuma an basu kulawar data kamata.
Hattara, Hukumar NAFDAC ta yi gargadi ga wanda basu son daukar ciki, inda tace an shigo da Maganin hana daukar ciki na Boge Najeriya, Ji yanda zaku ganeshi

Hattara, Hukumar NAFDAC ta yi gargadi ga wanda basu son daukar ciki, inda tace an shigo da Maganin hana daukar ciki na Boge Najeriya, Ji yanda zaku ganeshi

Duk Labarai
Hukumar kula da magunguna da abinci ta kasa, NAFDAC ta yi gargadi cewa an shigo da maganin hana daukar ciki me suna Postinor na bogi Najeriya. Hukumar tace ta tabbatar da hakan ne bayan da hukumar Society for Family Health (SFH) wadda itace aka yadda ta shigo da maganin ta bayyana cewa ba itace ta shigo da maganin boge din ba. NAFDAC tace yanda za'a gane maganin na boge shine, rubutunsa kanana ne, sannan an yi kuskuren rubuta kalmar Verify inda aka rubuta Veify. Sannan kuma akwai kuskuren rubutun Distnibuted in Nigeria maimakon a rubuta, distributed in Nigeria. Hukumar tace wannan magani na jabu na nan yana yawo a Najeriya kuma akwai yiyuwar yana dauke da sinadarai masu cutarwa dan haka ta nemi a gujeshi.
Kalli Yanda a Maulidin Bana, Sheikh Qaribu Kabara Ya kawo tsarabar Reshen Itaciyar Annabi Adamu(AS)

Kalli Yanda a Maulidin Bana, Sheikh Qaribu Kabara Ya kawo tsarabar Reshen Itaciyar Annabi Adamu(AS)

Duk Labarai
Bishiyar Annabi Adamu A.S. Tsarabar Mawloudin Bana a gidan Qadiriyya ita ce, reshen Bishiyar Itaciyar Annabi Adamu A.S.Bayan an yi bukin ɗaga tuta an fara baje kolin kayan tarihi a gidan sakamakon shiga bukin maulidin a Kano. Inda aka gano Qaribu Kabara tare da rike wani Reshe da ake cewa reshen bishiyar Annabi Adamu ne da aka kawo masa daga kasar Saudiyya a matsayin kyautar bangirma saboda haɗinkan da ya bayar wajen daƙile Sheikh Abduljabbar Kabara ɗan uwansa da ake zargin zai shiga Shi'a.Rahoton: Shawus Assufy NaTa'ala Me za ku ce!
Mun kulla huldar kudi, harkar lafiya, Sufuri da kasar Brazil>>Inji Shugaba Tinubu

Mun kulla huldar kudi, harkar lafiya, Sufuri da kasar Brazil>>Inji Shugaba Tinubu

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayyana cewa, Najeriya da kasar Brazil sun kulla huldar kasuwanci data hada da Kudi, Harkar lafiya, da sufuri da kuma huldar diflomasiyya. Ya bayyana hakane a shafinsa na sada zumunta inda yace a yanzu sun kulla huldar tashin jirage daga Najeriya zuwa kasar Brazil Kai tsaye. Sannan akwai maganar kimiyya da fasaha da sauransu.
Kalli Bidiyo: Akwai wanda yace mana idan Izala Gaskiya ce kada Allah yasa ya kai shekara me zuwa, kuma baikai labari ba, kamin shekara ta zagayo ya riga mu gidan gaskiya>>Inji Sheikh Yusuf Sambo Rigachukun

Kalli Bidiyo: Akwai wanda yace mana idan Izala Gaskiya ce kada Allah yasa ya kai shekara me zuwa, kuma baikai labari ba, kamin shekara ta zagayo ya riga mu gidan gaskiya>>Inji Sheikh Yusuf Sambo Rigachukun

Duk Labarai
Malamin Addinin Islama, Sheikh Yusuf Sambo Rigachukun ya bayar da labarun irin mutanen da ya kara dasu a baya kuma basu kai labari ba. Malam yace daga cikinsu akwai wanda yace idan Izala Gaskiyace kada Allah ya kaishi shekara me zuwa kuma baikai shekarar me zuwa ba. Malam ya bayyana hakane a wajan tafsir da yake yi. https://www.tiktok.com/@saleemyusufmuhammadsambo/video/7541886797857426695?_t=ZS-8zCarB4l1tI&_r=1
Kalli Bidiyon abinda wata dalibar jami’a tawa malaminta saboda ya kwace mata waya bayan kamata tana satar amsa, da yawa sun ce tarbiyya ta lalace

Kalli Bidiyon abinda wata dalibar jami’a tawa malaminta saboda ya kwace mata waya bayan kamata tana satar amsa, da yawa sun ce tarbiyya ta lalace

Duk Labarai
Wata daliba a jami'ar Niger Delta University dake jihar Bayelsa ta kama malaminta da fada bayan da ya kwace mata waya saboda kamata tana satar amsa. Rahotanni dai sun ce dalibar ta fara dukan malaminta inda shima ya zage ya rama. A Bidiyon da ya yadu sosai a kafafen sada zumunta an ga Malamin shima ya dage yana dukar dalibar. https://twitter.com/dammiedammie35/status/1959999856295989379?t=x-kuJAwxEllVbygVlbWqZw&s=19
Kalli Karin Hotuna da Bidiyo daga faduwar da jirgin kasan dake jigila tsakanin kaduna zuwa Abuja yayi a yau

Kalli Karin Hotuna da Bidiyo daga faduwar da jirgin kasan dake jigila tsakanin kaduna zuwa Abuja yayi a yau

Duk Labarai
A dazu ne muka ji labarin cewa, jirgin kasar dake jigila tsakanin Kaduna zuwa Abuja ya fadi bayan ya taso daga Abuja. Zuwa yanzu dai babu sanarwar ko an ji rauni ko asarar dukiya ko ta rai. Bidiyo ya bayyana na yanda lamarin ya faru. https://twitter.com/_UncleDara/status/1960345192990404899?t=AMYO3G8AkF4U5W_ujH3u7A&s=19 https://twitter.com/TheNationNews/status/1960322832262410424?t=BcRiUZrk37MHuHuLxYC_Kw&s=19
Mayar da takarar Shugaban kasa na PDP zuwa kudu, kokari ne na taimakon Tinubu ya ci zabe>>Inji Gbenga Olawepo-Hashim

Mayar da takarar Shugaban kasa na PDP zuwa kudu, kokari ne na taimakon Tinubu ya ci zabe>>Inji Gbenga Olawepo-Hashim

Duk Labarai
Tsohon dan takarar shugaban kasa kuma jigo a jam'iyyar PDP, Gbenga Olawepo-Hashim ya zargi jam'iyyar PDP din da yunkurin taimakin Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya sake cin zabe. Ya bayyana hakane bayan da jam'iyyar PDP tace dan kudu zata tsayar takarar shugaban kasa inda Gbenga yace hakan yunkuri ne na taimakawa Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya ci zabe a 2027. Ya bayyana hakane a yayin hirar da aka yi dashi a Channels TV inda yace masu neman a tsayar da dan kudu takarar shugaban kasar irin wanda suka raba kafa ne a PDP suna cewa, suna tare da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu amma kuma suna cikin PDP.
Tun da na hau mulki cin hanci ya zama tarihi a Nijeriya – Tinubu

Tun da na hau mulki cin hanci ya zama tarihi a Nijeriya – Tinubu

Duk Labarai
Tun da na hau mulki cin hanci ya zama tarihi a Nijeriya - Tinubu Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya tabbatar wa masu saka hannun jari na kasar Brazil cewa gyare-gyaren tattalin arzikin da ake aiwatarwa a Najeriya suna samar da ingantattun sakamako, inda ya yi ikirarin cewa “ba a sake samun cin hanci da rashawa ba” tun bayan da ya hau kujerar shugaban kasa. Jaridar Tribune ta rawaito cewa Shugaban ya bayyana hakan ne a yayin wani taro da aka gudanar a ranar Litinin tare da ministoci daga kasashen biyu da kuma mambobin kungiyar kasuwanci ta Brazil, inda ya sake jaddada shirye-shiryen Najeriya na karfafa hadin gwiwa a bangaren fasahar zamani, samar da abinci, masana’antu da makamashi. Tinubu ya bayyana tattalin arzikin Najeriya a matsayin “wata babbar kasuwa mai dimbin damammak...
Akwai yiwuwar samun ambaliya a jihohin Borno, Jigawa da Yobe – Nimet

Akwai yiwuwar samun ambaliya a jihohin Borno, Jigawa da Yobe – Nimet

Duk Labarai
Akwai yiwuwar samun ambaliya a jihohin Borno, Jigawa da Yobe, kamar yadda Hukumar Yanayi ta Najeriya (NiMet) ta sanar a wani hasashen yanayi da ta fitar a shafinta na X. Hukumar ta ce tsawa da ruwan sama matsakaici na iya sauka a wasu sassan arewacin Najeriya wadda zai iya haddasa ambaliyar ruwan. NiMet ta bayyana cewa da safiyar yau Talata, ana sa ran ruwan sama a jihohin Borno, Yobe, Jigawa, Gombe, Bauchi, Adamawa, Kaduna da Taraba. Hakanan, da yamma zuwa dare, ana sa ran yawancin jihohin Arewa za su ci gaba da samun ruwan sama tare da iska da tsawa. A tsakiyar Najeriya kuwa, hasashen ya nuna cewa za a samu yanayin giragizai da safe, sannan da yamma za a samu ruwan sama matsakaici a wasu sassan Nasarawa, Benue, Kogi, Kwara, Neja, Filato da kuma babban birnin tarayya Abuja. ...