Tuesday, December 16
Shadow

Duk Labarai

Ba sai kun sha Kwàyà ba zaku iya aiki>>Hukumar Sojojin Najeriya ta gargadi kananan sojojin

Ba sai kun sha Kwàyà ba zaku iya aiki>>Hukumar Sojojin Najeriya ta gargadi kananan sojojin

Duk Labarai
Hukumar sojojin Najeriya ta gargadi kananan sojoji cewa, ba sai sun sha kwaya ba zasu iya aiki yanda ya kamata. Kwamandan rundunar sojojin Najeriya ta 17 dake jihar Katsina, B.O. Omopariola ne ya bayyana haka a yayin wani tron karawa juna sani da aka gudanarwa sojojin kan matsalar tsaro. Jami'an hukumar yaki da safarar miyagun Kwàyòyì NDLEA sun halarci taron inda suka wayarwa da sojojin kai game da hadarin ta'ammuli da miyagun kwayoyin. B.O. Omopariola ya bayyana cewa bai yadda sai soja ya sha kwaya sannan zai iya aiki ba, yace sun yaki 'yan ta'dda sosai amma babu sojan da yayi amfani da kwaya a lokacin. Yace dan haka kada wani ya kawo mai maganar sai an sha kwaya sannan za'a iya aiki.
Da Duminsa: Gwamnan Filato ya tona asirin wadanda suka kirkiri matsalar tsaro a Najeriya

Da Duminsa: Gwamnan Filato ya tona asirin wadanda suka kirkiri matsalar tsaro a Najeriya

Duk Labarai
Gwamnan jihar Filato, Caleb Mutfwang ya bayyana cewa manyan mutane masu fada aji a kasarnan ne suka kirkiri matsalar tsaro a Najeriya. Ya bayyana hakane a wajan wani taro inda aka tattauna matsalar tsaro a jihar Filato ranar Laraba inda ya zargi masu fada aji da kawo matsalar tsaro a jiharsa. Yace wadanda suka kirkiri matsalar zasu iya magance matsalar tsaron idan suka ga dama. Yace idan irin wadannan manyan mutanen suka hada kai dan jagorancin mutane ta hanyar da bata kamata ba, za'a ci gaba da fuskantar matsalar tsaro duk shekara. Yace masu fada ajinne ke kara ruruta wutar rikicin ta hanyar zuga mutane akan ci gaba da rikicin. Ya jawo hankalin cewa, masu fada aji ya kamata suna karfaa zaman lafiya ne tsakanin al'umma.
Sabbin Motocin jigilar man fetur da muka kawo zasu samar da ayyuka 15000>>Dangote

Sabbin Motocin jigilar man fetur da muka kawo zasu samar da ayyuka 15000>>Dangote

Duk Labarai
Matatar man fetur ta Dangote tace sabbin motocin jigilar man fetur data kawo guda 4000 zasu samar da ayyukan yi na kai tsaye guda 15,000. Matatar tace mutanen da zasu samu ayyukan sun hada da Direbobi da manajoji da sauransu. Matatar man fetur din tace ta kashe Naira Biliyan 720 wajan sayo wadannan motocin jigilar man fetur din. Matatar tace zata kashw naira Tiriliyan N1.07 waja rabon man fetur din a shekara. Tace nan da 15 ga watan Augusta zata fara raba man zuwa gidajen man fetur da manyan masana'antu da sauran manyan masu amfani da man fetur a fadin Najeriya. Matatar tace wannan tsari zai amfani kananan masana'antu guda miliyan 42.
BABBAN MAGANA: Wani dan kasar Israila ya mutu a Abuja

BABBAN MAGANA: Wani dan kasar Israila ya mutu a Abuja

Duk Labarai
BABBAN MAGANA: Wani dan kasar Israila ya mutu a Villa. Ana bincike kan mutuwar wani dan kasar Israila mai shekara 73, Avi Warshaviak, wanda ya mutu a wani Otel mai suna "Corinthia Villa Hotel" dake Garki a Abuja babban birnin tarayyar Najeriya Bayanai sun nuna mutumin ya kama otel din sai kuma ya fara rashin lafiya kafin ayi wani abu akai har ya mutu Yanzu menene abun yi? ~A Yau
Kwankwaso yaci amanarmu mun barwa APC shi, inji jam’iyyar NNPP

Kwankwaso yaci amanarmu mun barwa APC shi, inji jam’iyyar NNPP

Duk Labarai
DA DUMI-DUMI: Kwankwaso yaci amanarmu mun barwa APC shi, inji jam'iyyar NNPP. Jam’iyyar NNPP ta bayyana cewa zai zama babban farin ciki a gare ta idan dan takararta na shugaban kasa a zaben 2023, Rabiu Musa Kwankwaso, ya koma jam’iyyar mai mulki ta APC. Hakan na kunshe ne a wata sanarwa da Sakataren Jam’iyyar na Kasa, Mista Oginni Olaposi, ya fitar ranar Lahadi a Legas. Olaposi ya mayar da martani ne kan murabus din da Abdullahi Ganduje ya yi daga shugabancin APC da kuma jita-jitar cewa ya yi hakan ne domin ba wa Kwankwaso damar shiga jam’iyyar. “Kwankwaso ya ci amanar da muka ba shi ta hanyar kokarin kwace jam’iyyar daga hannun wanda ya kafa ta, Dokta Boniface Aniebonam, wanda ya ba shi damar samun tikitin takarar shugaban kasa kyauta a 2023,” in ji shi. ~ Hikima Radio ...
Haziƙin Babban Jami’in Sojan Nijeriya, Birgediya Janar AS Aliyu Wanda Ya Yi Nasarar Tsallakowa Daga Cikin Jirgin Sama A Lokacin Da Yake Tafiya A Sararin Samaniya, Wanda Kusan Wannan Shine Karo Na Biyu Da Wani Babban Jami’in Ya Samu Nasarar Yin Wannan Jarumtar

Haziƙin Babban Jami’in Sojan Nijeriya, Birgediya Janar AS Aliyu Wanda Ya Yi Nasarar Tsallakowa Daga Cikin Jirgin Sama A Lokacin Da Yake Tafiya A Sararin Samaniya, Wanda Kusan Wannan Shine Karo Na Biyu Da Wani Babban Jami’in Ya Samu Nasarar Yin Wannan Jarumtar

Duk Labarai
Haziƙin Babban Jami'in Sojan Nijeriya, Birgediya Janar AS Aliyu Wanda Ya Yi Nasarar Tsallakowa Daga Cikin Jirgin Sama A Lokacin Da Yake Tafiya A Sararin Samaniya, Wanda Kusan Wannan Shine Karo Na Biyu Da Wani Babban Jami'in Ya Samu Nasarar Yin Wannan Jarumtar
Sanata Natasha Ta Ci Karo Da Hoton Wannan Mutumin Ne Dauke Da Hular Da Aka Rubuta Sunanta A Jiki, Ganin Yadda Mutumin Ya Yi Kalar Tausayi, Hakan Ya Sa Ta Sa Aka Nemo Shi Ta Ba Shi Wani Kunshi Na Kudi

Sanata Natasha Ta Ci Karo Da Hoton Wannan Mutumin Ne Dauke Da Hular Da Aka Rubuta Sunanta A Jiki, Ganin Yadda Mutumin Ya Yi Kalar Tausayi, Hakan Ya Sa Ta Sa Aka Nemo Shi Ta Ba Shi Wani Kunshi Na Kudi

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Sanata Natasha Ta Ci Karo Da Hoton Wannan Mutumin Ne Dauke Da Hular Da Aka Rubuta Sunanta A Jiki, Ganin Yadda Mutumin Ya Yi Kalar Tausayi, Hakan Ya Sa Ta Sa Aka Nemo Shi Ta Ba Shi Wani Kunshi Na Kudi
Kalli Hadiza Gabon ta wallafa hotunan ta lokacin tana ‘yar Lukuta da yanzu data rame inda tace kula da jiki na da muhimmanci

Kalli Hadiza Gabon ta wallafa hotunan ta lokacin tana ‘yar Lukuta da yanzu data rame inda tace kula da jiki na da muhimmanci

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Tauraruwar fina-finan Hausa, Hadiza Gabon ta wallafa tsaffin hotunanta dana yanzu. Hadiza wadda ta jawo cece-kuce bayan data rame tace kula da jiki na da kyau dan farin cikin meshi.