Wednesday, March 4
Shadow

Duk Labarai

Masallata a masallacin kasar Turkiyya da aka sakawa sunan dan Kwallon Najeriya, Victor Osimhen sun ce basu yadda a sakawa masallacinsu sunan Kirista ba, dole a canja

Masallata a masallacin kasar Turkiyya da aka sakawa sunan dan Kwallon Najeriya, Victor Osimhen sun ce basu yadda a sakawa masallacinsu sunan Kirista ba, dole a canja

Duk Labarai
Masallata a masallacin Bulut Mosque dake kasar Turkiyya sun ce basu yadda da canjawa masallacinsu suna zuwa Victor Osimhen ba. Masallacin dai an ginashine a shekarr 2008 inda aka saka masa sunan Bulut. Abinda ya faru shine a Google, idan ka duba masalacin zaka ga sunansa Victor Osimhen Mosque. Saidai masallatan dake Sallah a masallacin sun ce Dan kwallon bai taba amfanar masallacin da komai ba sannan bai taba amfanar garinsu da komai ba dan haka basu yadda da wannan ba, bugu da kari gashi kirista ne. Wasu dai na ganin cewa, kuskurene aka samu wajan rubutu da ya kawo hakan.
Kalli Bidiyo: Mutane na ta Mun sharrin wai Qaruwanci na yi aka bani motar GLK, ni kuma wallahi ban ma taba haduwa da wanda ya bani ba>>Inji Rahama Sa’idu

Kalli Bidiyo: Mutane na ta Mun sharrin wai Qaruwanci na yi aka bani motar GLK, ni kuma wallahi ban ma taba haduwa da wanda ya bani ba>>Inji Rahama Sa’idu

Duk Labarai
Tauraruwar Tiktok, Rahama Sa'idu ta bayyana cewa abinda mutane ke fadi akanta wanda ba daidai ba shine wai ita karuwace. Tace musamman sanda aka bata kyautar Motar GLK, tace da yawa na cewa wai ta bayar da kantane. Tace amma abinda mutane basu sani ba shine wanda ya bata motar bata taba ganinshi ba. Tace suna dai waya, yana ce mata zai je sayen takalma dan ita abinda take sayarwa kenan. Kalli Bidiyon anan
Maimakon Miliyan 10 da yayi Alkawarin baiwa tauraron Kannywood, Jamilu Kochila a matsayin gudummawar Aurensa, Dan kasuwa, Baballe Na’abba yace a yanzu zai basu kujerar makka da Madina

Maimakon Miliyan 10 da yayi Alkawarin baiwa tauraron Kannywood, Jamilu Kochila a matsayin gudummawar Aurensa, Dan kasuwa, Baballe Na’abba yace a yanzu zai basu kujerar makka da Madina

Duk Labarai
A lokacin bikin Tauraron Kannywood, Jamilu Kochila, da yawa sun yi alkawarin bashi gudummawa amma basu cika Alkawari ba. Daga cikin cikin wadanda suka yi wannan alkawarin, akwai dan Kasuwa, Baballe Na'abba wanda yayi Alkawarin bayar da gudummawar Naira Miliyan 10. Saidai daga baya a yanzu yace zai baiwa Amarya da Ango kujerun zuwa Makkah da Madina. Mansurah Isah ce ta bayyana hakan.
Da duminsa: Hukumar EFCC na tsare da tsohon gwamnan Sokoto, Tambuwal kan badakalar Naira Bilyan 189.

Da duminsa: Hukumar EFCC na tsare da tsohon gwamnan Sokoto, Tambuwal kan badakalar Naira Bilyan 189.

Duk Labarai
Da duminsa: Hukumar EFCC na tsare da tsohon gwamnan Sokoto, Tambuwal kan badakalar Naira Bilyan 189. EFCC TA Garƙame Tambuwal A Abuja Wakiliyarmu Khubrah Mustapha Dabai A halin yanzu dai tsohon gwamnan jihar Sokoto, Aminu Tambuwal yana hannun hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa ta EFCC a hedikwatarta da ke Abuja. Ana yi wa Tambuwal tambayoyi ne kan zarge-zargen fitar da makudan kudade da suka kai Naira biliyan 189, wanda aka bayyana a fili cewa yin hakan ya saɓawa dokar halatta kudaden haram, ta shekarar 2022. Majiyarmu ta talabijin ta tattaro cewa tsohon gwamnan ya isa ofishin EFCC ne da misalin karfe 11:30 na safe, inda aka kai shi gaban kwamitin bincike kan badakalar kuɗaɗen. Duk ƙoƙarin da Dimokuradiyya Tv ta yi har zuwa lokacin hada wannan rah...
Makusancin Kwankwaso, Abulmumin Kofa, ya gana da Tinubu karo na biyu cikin makonni biyu

Makusancin Kwankwaso, Abulmumin Kofa, ya gana da Tinubu karo na biyu cikin makonni biyu

Duk Labarai
Makusancin Kwankwaso, Abulmumin Kofa, ya gana da Tinubu karo na biyu cikin makonni biyu. Abdulmumin Jibrin Kofa, makusanci ga Rabiu Musa Kwankwaso na NNPP, ya sake ganawa da Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu a fadar Aso Villa, Abuja, a ranar Lahadi — karo na biyu cikin makonni biyu. Rahotanni sun nuna cewa ganawar ta dauki tsawon sa’o’i biyu, inda ake kyautata zaton ta shafi dangantakar Tinubu da Kwankwaso da kuma karuwar adawa ga jam’iyyar APC a wasu yankunan arewacin Najeriya. Jibrin, wanda ya ki bayyana dalilin tattaunawar, ya yi ganawa ta farko da Tinubu a ranar 30 ga Yuli, inda ya ce sun tattauna kan dunkulewar kasa da ci gaban ta. Ganawar ta na zuwa ne kwanaki bayan zargin Kwankwaso cewa gwamnatin tarayya na fifita kudu a ayyukan ci gaba. Wasu majiyoyi daga fadar shu...
‘Jihohin arewa huɗu ne kawai suke biyan mafi ƙarancin fansho na N32,000’

‘Jihohin arewa huɗu ne kawai suke biyan mafi ƙarancin fansho na N32,000’

Duk Labarai
Ƙungiyar ƴan fansho na arewacin Najeriya, NUP ta ce jihohi huɗu cikin 19 na arewacin Najeriya ne kaɗai suke biyan mafi ƙarancin fanshon naira 32,000 da gwamnatin tarayya ta tsara. Da yake bayani a taron shiyya na ƙungiyar a Kaduna, shugaban ƙungiyar, Kwamrade Mohammed Sali ya bayyana lamarin da "rashin adalci" da ya ce ake yi wa tsofaffin ma'aikatan bayan sadaukar da rayuwarsu da suka yi wajen aikin al'umma, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito. "Jihohi huɗu ne kacal ke biyan mafi ƙarancin fansho na naira 32,000 a arewacin Najeriya mai jihohi 19. Akwai jihohin da suke biyan fanshon naira dubu 3,000 da 4,000 da 5,000," in ji shi, inda ya ƙara da cewa ƙungiyar za ta fi mayar da hankali kan neman hanyoyin sasanci maimakon fito na fito da gwamnatocin jihohin. "Ba za mu...
Mutane Miliyan 1.9 ne suka nemi aikin Fire Service, Immigration, da Civil Defence da aka bude kwanannan, yayin da mutane dubu 30 ne kadai za’a dauka, Kalli Yawan mutanen da suka nema daga kowace jiha

Mutane Miliyan 1.9 ne suka nemi aikin Fire Service, Immigration, da Civil Defence da aka bude kwanannan, yayin da mutane dubu 30 ne kadai za’a dauka, Kalli Yawan mutanen da suka nema daga kowace jiha

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":["local"],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} An fitar da Alkaluman bayanai kan yawan mutanen da suka nemi aiki a Hukumomin Civil Defence, Fire Service, da Immigration. Tuni dai aka kulle shafin bayan kammala daukar aikin. Sannan an fitar da bayanai kan yawan wadanda suka nemi aikin wadanda suka kai mutane 1,910,539. Jihohi 5 da suka fi mutane da yawa da suka nemi aikin sune: Kogi State- 116,124 Kaduna- 114,500 Benue- 110,525 Kano- 89,355 Niger- 79,504 Jihohin da ke da mutane mafiya karanci da su...
Da Duminsa: Gwamnatin Tarayya zata gudanar da tantance ma’aikatan gwamnati dan korar na bogi da wadanda suka sayi ayyuka, ji bayani dalla-dalla

Da Duminsa: Gwamnatin Tarayya zata gudanar da tantance ma’aikatan gwamnati dan korar na bogi da wadanda suka sayi ayyuka, ji bayani dalla-dalla

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Gwamnatin tarayya zata gudanar da sabuwar tantance ma'aikatanta dan fitar da bara gurbi. Za'a yi tantancewar ma'aikatan ne da aka dauka daga shekarar 2013 zuwa shekarar 2023. Babbar sakatariya a ma'aikatar kula da ma'aikatan Gwamnatin tarayya (FCSC), Ndiomu Ebiogeh Philip ta bayyana cewa a wannan karin ba za'a daga yin tantancewar ba kuma duk wanda bai je an tantanceshi ba, za'a bayyanashi a matsayin wanda bai da takardar daukar aiki me kyau za'a sallameshi daga aiki. Hakan na zuwane a yayin da ake ta siyan aiki da kudi kuma ana zargin takardar aiki da ake baiwa irin wadanda suka sayi aikin ba me kyau bace.
Kalli Bidiyo: Dan Allah a bar kade-kade da sunan yabon Annabi(Sallallahu Alaihi Wasalam) bashi da asali a addini>>Inji Sheikh Maqari

Kalli Bidiyo: Dan Allah a bar kade-kade da sunan yabon Annabi(Sallallahu Alaihi Wasalam) bashi da asali a addini>>Inji Sheikh Maqari

Duk Labarai
Babban malamin Addinin Islama, Sheikh Ibrahim Maqari ya nemi a daina kade-kade da sunan yabon Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam). Malam ya bayyana cewa hakan bashi da asali a addini. Malam ya bayyana cewa yabon Annabi wanda ba kida yafi. https://www.tiktok.com/@kwanyawa.boy/video/7528095288674766136?_r=1&u_code=ejaikd8elj8058&preview_pb=0&sharer_language=en&_d=ejaij098emc1h5&share_item_id=7528095288674766136&source=h5_m&timestamp=1754904341&user_id=7483197776647635989&sec_user_id=MS4wLjABAAAAN7fVbcc0mzRzgIxdVwTekj-Bzgfq381B8aILPWs15fqP6aFNZ5GwIpbLEwMTYvVW&social_share_type=0&utm_source=copy&utm_campaign=client_share&utm_medium=android&share_iid=7510327615027545862&share_link_id=3cf7636a-432c-4fba-a6fa-f5bd6a99f3b6&sh...