Wednesday, March 4
Shadow

Duk Labarai

‘Ba za mu ɗamunci ɗabi’ar da za ta taɓa ƙimar gwamnatinmu ba’

‘Ba za mu ɗamunci ɗabi’ar da za ta taɓa ƙimar gwamnatinmu ba’

Duk Labarai
Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya gargaɗi masu riƙe da madafun iko a gwamnatinsa. A lokacin taron majalisar zartarwar jihar, Abba gida-gida ya buƙaci mambobin majalisar zartarwarsa su yi aiki bisa ƙwarewa da mutunta aikinsu. Gargaɗin na zuwa ne bayan ritayar kwamishinan sufuri na jihar, Ibrahim Namadi kan zarginsa da hannu a belin Danwawu, mutumin da ake zargi da safarar miyagun ƙwayoyi a jihar. “Bari na gaya muku gaskiya, ba za mu lamunci duk wata ɗabi'ar da za ta taɓa ƙimar gwamnatinmu ba, don haka dole kowane mai riƙe da muƙami ya lura da kyau kan abubuwan da zai yi,'' in ji shi. Gwamnan ya ce masu riƙe da muƙamai a gwamnatinsa ba ofishinsu kawai sukee wakilita ba, suna wakiltar duka gwamnatin ne. ''Mun zo gwamnati ne da nufin tsaftace tarbiyya da inganta rayuwar al...
Ana tsare da Sowore cikin tasku da cin zarafi – Lauyoyinsa

Ana tsare da Sowore cikin tasku da cin zarafi – Lauyoyinsa

Duk Labarai
Lauyoyin ffitaccen ɗan gwagwarmayar nan kuma ɗan jarida, Omoyele Sowore da hukumomin ƙasar ke tsare da shi ya yi kiran sakinsa cikin gaggawa. Lauyoyin sun yi zargin cewa ana tsare da Sowore ƙarƙashin kulawar babban sifeton ƴansandan ƙasar, cikin hali maras kyau na tasku da cin zarafinsa, lamarin da suka ce yana barazana ga kariyarsa. A ranar Laraba ne dai aka bayar da rahoton tsare Sowore bayan da ya amsa gayyatar jami'an ƴansanda domin amsa wasu tambayoyi. Ɗaya daga cikin lauyoyin nasa da ya zanta da sashen Pidgin na BBC, Marshal Abubakar ya ce an gayyacci Sowore ne kan zarge-zargen laufukan bata suna da yin ƙaryar takardun ƴansanda. Ya ce ƴansanda sun nuna musu wasu takardu na ƙorafi da aka rubuta kan Soworen, yana mai zargin ƴansanda da rubuta ɗaya daga ciki ƙorafe-ƙorafen. ...
Da Duminsa: ‘Yansanda sun gano Bama-Bamai da aka ajiye a cikin Bola a Kaduna

Da Duminsa: ‘Yansanda sun gano Bama-Bamai da aka ajiye a cikin Bola a Kaduna

Duk Labarai
Rahotanni daga Kaduna na cewa 'yansandan jihar sun gano wani bam da aka ajiyeshi a Bola a jihar. Kakakin 'Yansandan jihar, Mansir Hassan ya tabbatar da hakan a wata sanarwa da ya fitar. Yace an gano bam dinne a cikin wasu karikitai irin na masu jari bola a wani kanfanin sarrafa kayan bolar dake unguwar Kudenden. Yace Bom din na cikin karikitan bola ne da aka dauko daga Borno zuwa Kaduna. Yace tuni 'yansanda na musamman da suka iya kwance bom suka je wajan. Yace bayan bincike an tabbatar da cewa, bam ne wanda bai tashi ba a cikin karikitan. sannan an gano jarin makamai da suka hada da Bindiga da albarusai. Yace an kulle kamfanin har sai an kammala kawar da kayan makaman.
Akwai yiyuwar Najeriya zata tarwatse kamin shekarar 2027>>Inji Nwodo

Akwai yiyuwar Najeriya zata tarwatse kamin shekarar 2027>>Inji Nwodo

Duk Labarai
Tsohon Ministan yada labarai kuma tsohon shugaban kungiyar kare muradun Inyamurai, Chief John Nnia Nwodo yayi gargadin Najeriya na iya tarwatsewa kamin shekarar 2027. Ya bayyana hakane a Abuja wajan kaddamar da wani littafin a dakin taro na Shehu Musa 'Yar'adua ranar Laraba. Nwodo yace tsarin da ake kai ba zai kai Najeriya ga ci ba, yace dole a canja fasalin kasarnan. Ya bayyana cewa a canja kundin tsarin mulki kowane yanki a bashi dama ya rika cin gashin kansa yana biyan gwamnatin tarayya haraji. Yace amma idan ba haka ba, wasu yankin ba zasu yi zabe ba sannan wasu zasu nemi ballewa daga Najeriya.
Yanzu-Yanzu: Tsohon Shugaban kasa, Goodluck Jonathan ya amince ya tsaya takarar shugabab kasa a shekarar 2027

Yanzu-Yanzu: Tsohon Shugaban kasa, Goodluck Jonathan ya amince ya tsaya takarar shugabab kasa a shekarar 2027

Duk Labarai
2027: Jonathan zai tsaya takarar shugaban ƙasa don fafatawa da Tinubu. Tsohon shugaban ƙasa, Dr. Goodluck Jonathan, ya amince da tsayawa takarar shugabancin ƙasa a 2027, in ji wani amintaccen na jikinsa da ke cikin jam’iyyar PDP. Vanguard ta rawaito cewa na jikin ma Jonathan ya ce, an kai matakin karshe wajen shawo kan Jonathan da ya tsaya takara domin farfaɗo da tattalin arziki da rage wahalhalun jama’a. Majiyar ta bayyana cewa shirin dawowar Jonathan yana samun goyon bayan manyan shugabanni da dattawan ƙasa waɗanda suka yarda cewa mulkinsa na baya ya kwantar da tarzoma kuma ya daidaita tattalin arziki. An bayyana cewa Jonathan ya gana da tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida (mai ritaya), da kuma wasu manyan 'yan siyasa na Arewa da Kudancin ƙasar don neman goyon b...
Abin mamaki ne yayin da Miliyoyin ‘yan Najeriya ke cikin matsananciyar yunwa amma Shugaba Tinubu ya ware Naira Biliyan 712 dan gyaran filin jirgin sama>>Inji Peter Obi

Abin mamaki ne yayin da Miliyoyin ‘yan Najeriya ke cikin matsananciyar yunwa amma Shugaba Tinubu ya ware Naira Biliyan 712 dan gyaran filin jirgin sama>>Inji Peter Obi

Duk Labarai
Dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar Labour Party, Peter Obi ya bayyana cewa, abin Takaici ne irinnyanda shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya ware Naira Biliyan 712 dan gyaran filin jirgin sama a yayin da Miliyoyin 'yan Najeriya ke fama da yunwa. Yayi wannan maganane a yayin da Majalisar Dinkin Duniya ke gargadin cewa mutane Miliyan 34 a Najeriya na cikin hadarin fadawa matsalar yunwa. Peter Obi yace mutanen da Yunwa kewa barazana 'yan uwan mu ne, makwabtan mu ne kuma abokan mu ne, yace abin takaici shine a irin wannan hali ne gwamnati zata ware biliyoyin Naira ba dan ciyar da talaka ba sai dan gyaran filin jirgin sama. Obi yace a shekarar 2013 An ranto dala Miliyan 500 inda aka gyara manyan filayen jiragen saman Najeriya, dake Lagos, Abuja, Kano, Port Harcourt, da Enugu. Yace...
Gwamnatin Tarayya Ta Fara Shirin Farfaɗo da Masaku a Kaduna don Inganta Tattalin Arziki Da Ayyukan Yi

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Shirin Farfaɗo da Masaku a Kaduna don Inganta Tattalin Arziki Da Ayyukan Yi

Duk Labarai
Gwamnatin Tarayya Ta Fara Shirin Farfaɗo da Masaku a Kaduna don Inganta Tattalin Arziki Da Ayyukan Yi. Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta kaddamar da wani shiri na farfaɗo da masana’antun auduga, masaku da tufafi a ƙasar, inda ƙaramin Ministan Masana’antu, Kasuwanci da Zuba Jari, Sanata John Enoh, ya kai ziyara jihar Kaduna domin duba muhimman masana’antun da suka shafi bangaren. Ministan ya bayyana cewa sake farfaɗo da waɗannan masana’antu zai taimaka matuka wajen habaka tattalin arzikin ƙasa da samar da ayyukan yi ga matasa da ma sauran ’yan ƙasa. Bayan gudanar da wannan ziyara ta gani da ido, Sanata Enoh ya halarci wani taro tare da masu ruwa da tsaki domin tattaunawa kan hanyoyin da za a bi wajen dawo da martabar masana’antun sarrafa auduga da samar da tufafi a Najeriya. Ya ja...
Da yawan rukunin gidajen da aka yi watsi dasu a Abuja ma’aikatan gwamnati ne da suka saci kudi suke ginasu>>Inji EFCC

Da yawan rukunin gidajen da aka yi watsi dasu a Abuja ma’aikatan gwamnati ne da suka saci kudi suke ginasu>>Inji EFCC

Duk Labarai
Shugaban hukumar EFCC, Ola Olukoyede ya bayyana cewa, da yawan rukunin gidajen da aka fara ginawa aka bari dake Abuja, ma'aikatan gwamnati ne da suka saci kudade ke ginasu. Ya bayyana hakane a wajan wani taro da ya faru a Abuja ranar Laraba inda aka tattauna batun gidaje. Yace da yawa ma'aikatan gwamnati ne suke fara ginin amma idan suka ajiye aiki ba zasu iya ci gaba da ginin ba. Yace dan haka ya kafa kwamiti na musamman dan su rika bibiyar irin wadannan gidaje ana bincike wanda suka mallakesu da kuma ina suka samu kudin.