Thursday, March 5
Shadow

Duk Labarai

A yayin da aka baiwa ‘yan kwallo Najeriya Kyautar Naira Miliyan 150, Tsaffin sojoji sun fito kan tituna suna gangami a biyasu hakkokinsu

A yayin da aka baiwa ‘yan kwallo Najeriya Kyautar Naira Miliyan 150, Tsaffin sojoji sun fito kan tituna suna gangami a biyasu hakkokinsu

Duk Labarai
Tsaffin sojojin Najeriya sun fito zanga-zanga a yau Litinin dan neman a biyasu hakkokinsh a suke bin Gwamnati. Taffin sojojin da suka ajiye aiki tsakanin shekarun 2023 zuwa 2024 sun bayyana cewa ba'a musu adalci ba inda suka ce sun shafe shekaru suna aiki amma sun kammala biyan hakkokinsu ya gagara. Tsaffin sojojin sun gudanar da wannan zanga-zangar ne a ofishin ma'aikatar kudi ta tarayya. Hakan na zuwane yayin da Gwamnatin tarayya ke rabawa 'yan kwallo kyautar Miliyoyin Naira da gidaje.
Kalli Bidiyo:Yanda Farfesa Abudullah Uba Adamu yayi kacha-Kacha da Maryam Labarina kan ikirarin rashin yiwa miji Wanke-wanke

Kalli Bidiyo:Yanda Farfesa Abudullah Uba Adamu yayi kacha-Kacha da Maryam Labarina kan ikirarin rashin yiwa miji Wanke-wanke

Duk Labarai
Farfesa Abudallah Uba Adamu yayi Kacha-Kacha da Tauraruwar Kannywood, Maryam Labarina akan ikirarin ta na rashin son yiwa miji wanke-wanke. Farfesa Uba ya bayyana hakane a wajan wani jawabi daya gabatar Yace Toh akwai farfesoshi mata da yayi aiki dasu wadanda suke daraja martabar aure kuma basu fi karfin su yiwa mazajensu aiki ba. https://www.tiktok.com/@aka_abbaji/video/7534749870599671046?_t=ZS-8ybi0hepkO0&_r=1
Kalli Bidiyo: Wallahi Sheikh Kabir Gombe Kafirine kaima idan ka yi kokwanton hakan ka zama kafiri>>Inji Wannan Malamin

Kalli Bidiyo: Wallahi Sheikh Kabir Gombe Kafirine kaima idan ka yi kokwanton hakan ka zama kafiri>>Inji Wannan Malamin

Duk Labarai
Wannan wani sabon malami ne da ya bayyana yana kafirta malamai. Ya bayyana cewa, Sheikh Kabir Gombe Kafuri ne sannan duk ma wanda yayi kokwanton shima ya zama Kafiri. Yace yana da hujjojinsa kuma a shirye yake idan aka kirashi muqabala. https://www.tiktok.com/@student_yusuf_ismail__/video/7534690177575292165?_r=1&u_code=ejaikd8elj8058&preview_pb=0&sharer_language=en&_d=ejaij098emc1h5&share_item_id=7534690177575292165&source=h5_m&timestamp=1754344102&user_id=7483197776647635989&sec_user_id=MS4wLjABAAAAN7fVbcc0mzRzgIxdVwTekj-Bzgfq381B8aILPWs15fqP6aFNZ5GwIpbLEwMTYvVW&social_share_type=0&utm_source=copy&utm_campaign=client_share&utm_medium=android&share_iid=7510327615027545862&share_link_id=254ede0c-bd18-4a93-9960-4da00b4ed2...
YAN,U-YANZU: Gwamnan Kano Ya Buƙaci Mutumin Dake Shirin Tattaki Zuwa Wajensa Daga Jigawa Ya Koma Gida

YAN,U-YANZU: Gwamnan Kano Ya Buƙaci Mutumin Dake Shirin Tattaki Zuwa Wajensa Daga Jigawa Ya Koma Gida

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Gwamnan Kano Ya Buƙaci Mutumin Dake Shirin Tattaki Zuwa Wajensa Daga Jigawa Ya Koma Gida Gwamnan Kano ya yi kira ga wani masoyinsa da ke shirin tattaki zuwa wajensa a ƙafa daga Jigawa, Lawan Habib da ya yi zamansa a cikin iyalinsa ba sai ya zo ba. Gwamnan ta bakin mai magana da yawunsa, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ya ce addu'ar masoyin nasa yake buƙata ba jefa rayuwarsa cikin haɗari ba.
Matashiya ‘Yar Asalin Jihar Yobe, Nafisa Abdullahi Ta Lashe Gasar Turanci Ta Duniya

Matashiya ‘Yar Asalin Jihar Yobe, Nafisa Abdullahi Ta Lashe Gasar Turanci Ta Duniya

Duk Labarai
Matashiya 'Yar Asalin Jihar Yobe, Nafisa Abdullahi Ta Lashe Gasar Turanci Ta Duniya. Nafisa Abdullah Aminu, yarinya ‘yar shekaru 17 daga jihar Yobe, ta samu babban nasara a gasar ƙasa da ƙasa ta harshen Turanci da aka gudanar a London, Birtaniya, ƙarƙashin TeenEagle Global Finals 2025. Nafisa, wadda ke karatu a Nigerian Tulip International College (NTIC), Yobe, ta fice daga cikin fiye da ɗalibai 20,000 daga ƙasashe 69 – ciki har da waɗanda harshen Turanci ke matsayin na uwa-uba a wurinsu. Wannan gagarumar nasara da ta samu ana kallonta a matsayin abin alfahari ga Najeriya da nahiyar Afrika gaba ɗaya, duba da asalin jihar da ta fito wadda ke fama da ƙalubale a harkar ilimi da tsaro. A sakamakon haka, hukumomi da malamai a jihar Yobe sun nuna farin ciki da wannan nasara, suna...
Ina nan da raina, Samha M. Inuwa ta karyata rade-radin da ake yadawa akanta bayan hadarin data yi

Ina nan da raina, Samha M. Inuwa ta karyata rade-radin da ake yadawa akanta bayan hadarin data yi

Duk Labarai
Tauraruwar fina-finan Hausa, Samha M. Inuwa ta karyata rade-radin da ake yadawa na cewa ta mutu. Samha a sanarwar data fitar ta shafinta tace ta fito ta sanar da mutanene cewa, tana samun sauki kuma ba kamar yanda wasu ke yadawa ba cewa wai ta mutu, tace tana nan da ranta. Ta yi godiya da 'yan uwanta da abokan sana'arta da masoya da suka nuna damuwa game da abinda ya sameta. https://www.tiktok.com/@samha_m_inuwa/video/7534750431516380421?_t=ZS-8ybcxZqQPWT&_r=1
Kada ma ka yi tunanin tsayawa takarar shugaban kasa a 2027 dan ba zaka ci ba>>Wata Kungiyar Yarbawa ta gayawa shugaba Tinubu

Kada ma ka yi tunanin tsayawa takarar shugaban kasa a 2027 dan ba zaka ci ba>>Wata Kungiyar Yarbawa ta gayawa shugaba Tinubu

Duk Labarai
Wata Kungiyar Yarbawa me suna Ìgbìnmó Májékóbájé Ilé-Yorùbá ta bayyana cewa, Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya gaza a fannin inganta tattalin arziki da samar da tsaro. Kungiyar a sanarwar data fita daga bakin shugaban ta, Olusola Badero wanda me magana da yawunta, Princess Balogun ya fitar. Yace Talauci musamman a yankin Yarbawa ya karu hakanan matsalar tsaro ta karu. Ya kawo misalin cewa kwanannan aka sace wasu manoma a yankin inda sai da danginsu suka tara kudi sannan aka sakesu. Yace Tinubu ya kasa cika Alkawuran da ya dauka, dan haka yace Aso Rock ba gidan gado bane, kada ma Tinubu yayi tunanin tsayawa takara a 2027 dan ba ci zai yi ba.
WAEC ta fitar da sakamakon jarrabawar 2025

WAEC ta fitar da sakamakon jarrabawar 2025

Duk Labarai
Hukumar shirya jarrabawar kammala sakandire ta Afirka ta Yamma, WAEC ta fitar da sakamakon jarrabawar 2025 a Najeriya. Cikin wata sanarwa da hukumar ta wallafa a shafinta na X, ta ce ta saki sakamakon ne a yau Litinin 4 ga watan Agustan 2025. Hukumar ta kuma buƙaci ɗaliban da suka rubuta jarrabawar da su shiga shafinta na http://waecdirect.org. domin duba sakamakon jarrabawar tasu.
Suma ‘yan Kwallon Kwando mata Shugaba Tinubu ya baiwa kowaccensu kyautar Naira Miliyan 150 da gidaje

Suma ‘yan Kwallon Kwando mata Shugaba Tinubu ya baiwa kowaccensu kyautar Naira Miliyan 150 da gidaje

Duk Labarai
Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya ba ƴan wasan kwandon Najeriya mata dala 100,000 da lambar girma ta OON saboda nasarar da suka samu ta lashe kofin gasar kofin Afirka ta wato Afrobasket. Shugaban ya kuma ba masu horar da ƴanwasan dala 50,000 kowannensu. hakanan kowannensu an bata kyautar gida hadda masu horas dasu. Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ne ya bayyana hakan a madadin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu. Wannan na zuwa ne kwanaki kaɗan bayan shugaban ya ƴanwasan ƙwallon ƙafa mata kyautar dala 100,000 da lambar girma.