Saturday, December 13
Shadow

Duk Labarai

Zan iya mùtùwà a kan APC, in ji tsohon Gwamnan Abia, Uzor Kalu

Zan iya mùtùwà a kan APC, in ji tsohon Gwamnan Abia, Uzor Kalu

Duk Labarai
Tsohon Gwamnan Jihar Abia, Orji Uzor Kalu, ya sake jaddada cewa a shirye ya ke ya ba da ransa akan jam’iyyar APC, musamman a jihar Abia. Ya bayyana haka ne a hirarsa da manema labarai a garinsu na Igbere, Jihar Abia. Da aka tambaye shi ko APC na da wata dama ta kayar da jam’iyyar Labour Party (LP) a zaben 2027 a jihar Abia, Kalu wanda ke wakiltar Abia ta Arewa a Majalisar Dattawa, ya ce shi da sauran magoya bayan APC za su yi aiki tukuru domin nasarar shugaban kasa a jihar. Ya ce; “APC na da karfi a Abia. Kamar yadda na fada a wata hira, wla shirye nake in ba da raina saboda jam’iyyar. Ni mamba ne na APC kuma mai tsayawa kan gaskiyar jam’iyyar. Ni cikakken dan APC ne. Shi ya sa APC ke da karfi a Abia ta Arewa. “Jam’iyyarmu za ta yi aiki tukuru domin ganin shugaban kasa ya yi na...
Gwamnatin tarayya ta soke faretin bikin ranar dimokuraɗiyya

Gwamnatin tarayya ta soke faretin bikin ranar dimokuraɗiyya

Duk Labarai
Gwamnatin Tarayya ta soke faretin sojoji da ake yi don tunawa da Ranar Dimokuraɗiyya ta shekara-shekara, wadda za a gudanar da bikin ta a ranar Alhamis, 12 ga watan Yuni a matsayin cika shekara 26 da dimokuraɗiyya ta dawo Najeriya. Bayanan da Kwamitin Harkokin Bikin Ranar Dimokuraɗiyya na Ma’aikatu da dama ya fitar sun nuna cewa Shugaba Bola Tinubu zai yi jawabi ga al’ummar ƙasa baki ɗaya da misalin ƙarfe 7 na safe ranar Alhamis, ba tare da an gudanar da faretin Ranar Dimokuraɗiyya kamar yadda aka saba a baya ba. Maimaikon faretin, Shugaba Tinubu zai halarci zaman haɗin gwiwa na musamman da za a gudanar a Majalisar Tarayya da ƙarfe 12 na rana. Ana sa ran wannan zaman haɗin gwiwa zai ƙunshi jawaban da suka shafi halin da ƙasa ke ciki, tunawa da tafiyar dimokuraɗiyyar Najeriya, da k...
Natasha: Kotun Ɗaukaka Ƙara ta ci tarar Akpabio Naira dubu ɗari

Natasha: Kotun Ɗaukaka Ƙara ta ci tarar Akpabio Naira dubu ɗari

Duk Labarai
Kotun daukaka kara a Abuja ta yi watsi da bukatu guda biyu da Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya shigar, tare da yanke masa hukuncin biyan tara na naira 100,000. Kwamitin alkalai uku na kotun, wanda Mai Shari’a Hamman Barka ke jagoranta, ne ya yanke hukuncin a ranar 21 ga Mayu, 2025, bayan Akpabio ya nemi a janye karar da ya shigar. Kotun ta kuma tabbatar da sahihancin kwafin hukuncin. Bukatun da aka yi watsi da su an shigar da su ne a ranar 3 ga Maris, 2025, da kuma 25 ga Maris, 2025, kuma suna dauke da lambar shari’a CV/395/M1/2025 da CV/395/M2/2025, inda Akpabio ya kasance mai daukaka kara.
Bisa satar Naira miliyan 360, kotu ta yanke wa wani mutum hukuncin ɗaurin shekaru 74 a gidan yari

Bisa satar Naira miliyan 360, kotu ta yanke wa wani mutum hukuncin ɗaurin shekaru 74 a gidan yari

Duk Labarai
Wata babbar kotu da ke Ajah, a jihar Lagos, ta yanke wa Chukwudi Okonkwo Goodness, hukuncin daurin shekaru 74 a gidan yari bisa laifin satar Naira miliyan 360 da kuma bayar da takardun cirar kudi a asusun bankin da babu kuɗi a cikin sa. An gurfanar da Goodness ne a shekarar 2016 bisa tuhuma 33 da hukumar EFCC ta shigar. An ce ya karkatar da kuɗin ne daga wani mutum mai suna Henry Nnadike a Ikeja tsakanin watan Yuni da Yuli, 2015. Bayan shari’ar da ta ɗauki tsawon shekaru tara, mai shari’a Josephine Oyefeso ta same shi da laifi a kan tuhume-tuhume 32. Bayan haka an yanke masa hukuncin ɗaurin shekaru bakwai a kan tuhuma ta sata, sannan shekaru biyu-biyu a kowace tuhuma daga cikin sauran tuhume-tuhume da suka shafi bayar da katin cirar kudi a asusun da babu kuɗi a cikin sa. Haka z...
Bincike: Karanta Jadawalin jihohin da aka fi samun matan aure na aikata Zìnà, ‘yan mata ma na lalata, Rahoton yace babu irin wadannan matan ko daya a jihohin Jigawa, Katsina da Kebbi sannan Kuma jihar Taraba ce ta daya a Arewa wajan aikata wannan masha’a

Bincike: Karanta Jadawalin jihohin da aka fi samun matan aure na aikata Zìnà, ‘yan mata ma na lalata, Rahoton yace babu irin wadannan matan ko daya a jihohin Jigawa, Katsina da Kebbi sannan Kuma jihar Taraba ce ta daya a Arewa wajan aikata wannan masha’a

Duk Labarai
Wani rahoto daga kafar TheCable ya bayyana jihohin da aka fi samun matan aure da 'yan mata na aikata Zina da yawaitar karuwai. Rahoton yace an yi bincikene a kan 'yan mata masu shekaru tsakanin 15 zuwa 49. Rahoton yace a jihohin Jigawa, Katsina da Kebbi babu irin wadannan mata: Bayelsa: 28.5% Cross River: 23.9% Rivers: 23% Abia: 21.4% Delta: 22.1% Enugu: 20.3% Akwa-Ibom: 20.2% Edo: 20.1% Ondo: 19.9% Taraba: 19.9% Ekiti: 18.3% Benue: 16.8% Imo: 16.1% Lagos: 15.7% Osun: 15.2% Anambra: 14.9% FCT: 13.8% Plateau: 13% Kwara: 12.3% Oyo: 12.2% Ogun: 11.3% Kogi: 10.2% Nasarawa: 9.2% Ebonyi: 6.6% Adamawa: 5.6% Bauchi: 2.5% Gombe: 1.8% Kaduna: 1.7% Borno: 1.6% Niger: 1% Kano: 0.5% Zamfara: 0.5% S...
Kalli Bidiyon yanda aka rika jifar Sarki Sanusi Lokacin hawan Fanisau

Kalli Bidiyon yanda aka rika jifar Sarki Sanusi Lokacin hawan Fanisau

Duk Labarai
Rahotanni daga jihar Kano na cewa, an jefi sarki Muhammad Sanusi II a yayin hawan fanisau. Bidiyo ya karade kafafen sada zumunta inda aka ji wasu na fadar cewa an jefi sarkin. https://twitter.com/2027Apc/status/1932738745603928134?t=pHqm2Y0iKqvZSg4Ie3dEMA&s=19 Dubban masoya ne dai suka raka Sarki Sanusi Hawan Fanisau inda a wata majiyar ake cewa sun kai mutane Miliyan 5.
Ji yanda Kwaila ta gayawa Saurayinta Sojan Ruwa cewa Allah ya jefashi ruwa ‘yan ruwa su cinyeshi saboda ta tambayeshi dubu 1 be bata ba

Ji yanda Kwaila ta gayawa Saurayinta Sojan Ruwa cewa Allah ya jefashi ruwa ‘yan ruwa su cinyeshi saboda ta tambayeshi dubu 1 be bata ba

Duk Labarai
Wata kwaila ta dauki hankula a kafafen sada zumunta bayan da muryarta ta bayyana tana yiwa saurayinta wanda sojan ruwane rashin kunya. Kwailar dai ta nemi da ya bata dubu dayane bai bata ba inda tace masa Allah ya jefashi ruwa 'yan ruwa su cinyeshi. https://twitter.com/Ormarfaruq/status/1932346387225543142?t=wB4ld55-XMY7WDBPV4R0_w&s=19 Abin dai ya nishadantar.
Ka Yi Watsi Da Masu Suka, Ka Cigaba Da Ayyukan Cigaban Da Kake Yi, Sakon Tinubu Ga Wike

Ka Yi Watsi Da Masu Suka, Ka Cigaba Da Ayyukan Cigaban Da Kake Yi, Sakon Tinubu Ga Wike

Duk Labarai
Ka Yi Watsi Da Masu Suka, Ka Cigaba Da Ayyukan Cigaban Da Kake Yi, Sakon Tinubu Ga Wike. Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bukaci Ministan Abuja, Nyesom Wike, da ya ci gaba da aikinsa na alheri ba tare da sauraron masu suka ba. Tinubu ya bayyana hakan ne yau yayin kaddamar da sabun Dakin Taro na Ƙasa da Kasa da aka gyara kuma aka sake sanya mata suna Bola Ahmed Tinubu International Conference Centre a Abuja.
A karin farko: Kasashen Canada,UK, Australia da New Zealand zasu kakabawa kasar Israyla takunkumi saboda kìsàn Kiyashin da sukewa Falasdiynawa

A karin farko: Kasashen Canada,UK, Australia da New Zealand zasu kakabawa kasar Israyla takunkumi saboda kìsàn Kiyashin da sukewa Falasdiynawa

Duk Labarai
Kasashen Canada,UK, Australia da New Zealand zasu kakabawa wasu jami'an Gwamnatin kasar Israela 2 takunkumi. Wadanda za'a kakabawa wannan takunkumi sune Itamar Ben Gvir da Betzalel Smotrich wanda 'yan siyasa ne masu rura wutar ci gaba da kisan Falasdiynawa. Rahotanni a baya sun ce duka kasashe masu fada a ji na Duniya sun amince a dakatar da yakin Gaza in banda kasar Amurka. Dubban mutane ciki hadda mata da kananan yara ne aka kashe a Gàzà wanda kasashen Duniya ke cewa an aikata laifukan yaki.