Friday, December 19
Shadow

Duk Labarai

Mijinta ya kamata tana yiwa dan kishiyarta me shekaru 15 fyade, saidai duk da haka ta sake kiran yaron inda take tambayarshi ta gamsar dashi kuwa?

Mijinta ya kamata tana yiwa dan kishiyarta me shekaru 15 fyade, saidai duk da haka ta sake kiran yaron inda take tambayarshi ta gamsar dashi kuwa?

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa Mijin wannan matar wadda ma'aikaciyar Jinya ce ya kamata tana yiwa dansa, watau dan kishiyarta me shekaru 15 fyade. Lamarin ya sanya matar me shekaru 35 ta rasa lasisinta na aikin jinya. Rahoton yace matar ta kwashe kwanaki tana ta jan hankalin dan kishiyar tata, kamin daga bisani ta danneshi ta mai fyade. Alexis Von Yates na zaunene a jihar Florida ta kasar Amurka inda a yanzu take jiran zuwa watan July dan yanke mata hukuncin wannan aika-aika da ta yi. Ranar da abin zai faru matar baban nasa ta rika gaya masa cewa, tana jin sha'awa kuma bata yi juma'i ba na tsawon lokaci. Anan ne dai har suka kai ga aikata abinda suka aikata, bayan da babban ya dawo sai ya iskesu tsirara a kwance a falo. Anan ne ya dauki yaron ya mayar dashi gidan kakanninsa. ...
Ina Nan A Raye Amma Ba A Kulle Nake Ba, Batun Kamu Kuma A Koda Yaushe Za A Iya Kama Ni, Kuma A Shirye Nake Koda Zan Ŕàsà Raiña, Tunda Dama Sùn Jimà Suña Ñemañ Rabà Nì Da Rayùwațà, Kuma Ina Godiya Da Addù’o’inku Masoyana, Inji Odinari Ahmed Isa

Ina Nan A Raye Amma Ba A Kulle Nake Ba, Batun Kamu Kuma A Koda Yaushe Za A Iya Kama Ni, Kuma A Shirye Nake Koda Zan Ŕàsà Raiña, Tunda Dama Sùn Jimà Suña Ñemañ Rabà Nì Da Rayùwațà, Kuma Ina Godiya Da Addù’o’inku Masoyana, Inji Odinari Ahmed Isa

Duk Labarai
I na Nan A Raye Amma Ba A Kulle Nake Ba, Batun Kamu Kuma A Koda Yaushe Za A Iya Kama Ni, Kuma A Shirye Nake Koda Zan Ŕàsà Raiña, Tunda Dama Sùn Jimà Suña Ñemañ Rabà Nì Da Rayùwațà, Kuma Ina Godiya Da Addù'o'inku Masoyana, Inji Odinari Ahmed Isa.
Shugaba Tinubu Bai Sauke Ministocin Tsaron Nijeriya Ba – In ji Fadar Shugaban Ƙasa

Shugaba Tinubu Bai Sauke Ministocin Tsaron Nijeriya Ba – In ji Fadar Shugaban Ƙasa

Duk Labarai
Shugaba Tinubu Bai Sauke Ministocin Tsaron Nijeriya Ba - In ji Fadar Shugaban Ƙasa Mai magana da yawun shugaban kasar Bayo Onanuga ya ce masu yada irin wannan labarin na bogi, masu laifi ne da ya kamata a hukunta su ba tare da bata lokaci ba Wata kafar yada labarai ta zamani Phoenix browser ce dai ta fitar da labarin inda ta ce Shugaba Tinubu ya sallami minsitocin tsaro da kuma ministan lantarki
Sanata Natasha Akpoti ta kasa kawo hujjar cewa na nemeta da lalata shiyasa ta fara bani Hakuri, kumama inda zaku san sharri ne irin nasu na mata ta kulla min, bayan tace ne nemeta da lalata ta bini min je taruka da yawa har kasashen waje kuma har hotunan Selfie ta rika dauka dani>>Sanata Godswill Akpabio

Sanata Natasha Akpoti ta kasa kawo hujjar cewa na nemeta da lalata shiyasa ta fara bani Hakuri, kumama inda zaku san sharri ne irin nasu na mata ta kulla min, bayan tace ne nemeta da lalata ta bini min je taruka da yawa har kasashen waje kuma har hotunan Selfie ta rika dauka dani>>Sanata Godswill Akpabio

Duk Labarai
Kakakin majalisar Dattijai, Sanata Godswill Akpabio ya bayyana cewa Sanata Natasha Akpoti ta kasa kawo hujjojin kan zargin da take masa na cewa, ya nemeta da lalata. Ya bayyana hakane ta bakin lauyansa, Dr Olisa Agbakoba (SAN) yace dalili ma kenan na yin magamganin da ta yi kwanannan. Yace wani karin abin mamaki shine, Sanata Natasha Akpoti ta goge rubutun da ta yi na zargin da take masa a shafinta na sada zumunta. Yace wani karin abin dubawa shine Sanata Natasha Akpoti tace a shekarar 2023 ne Ya nemeta da lalata, amma bayan nan, ta bishi sun je taruka da yawa a ciki da wajen Najeriya a shekarar 2024. Yace a wajan wasu tarukan ma har hotunan Selfie take daukarsu tare kuma ta dora a kafafen sadarwa. Dan haka ya nemi Sanata Natasha Akpoti ta janye zargin da take masa.
Kalli Bidiyo: An zargi Gwamnati da hannu a tashin Gobarar kasuwar Taminus ta garin Jos

Kalli Bidiyo: An zargi Gwamnati da hannu a tashin Gobarar kasuwar Taminus ta garin Jos

Duk Labarai
A daren da ya gabata ne dai aka samu tashin Gobara a kasuwar Taminus ta garin Jos na jihar Filato. Daya daga cikin abinda mutane da yawa ke kokawa akai shine yanda jami'an kashe Gobara basu kai musu dauki da wuri ba. https://www.tiktok.com/@abasjos/video/7498904556814798085?_t=ZM-8vxlxzbBlSR&_r=1 Hakanan an koka kan yanda jami'an tsaro suke korar mutane daga wajan gobarar. Wani Bidiyo da ya watsu sosai a kafafen sada zumunta an ji wasu na zargin cewa akwai hannun gwamnati a lamarin.
Okowa dan gashi gareshi, shi ne dalilin da yasa Atiku ya fadi zabe a 2023>>PDP

Okowa dan gashi gareshi, shi ne dalilin da yasa Atiku ya fadi zabe a 2023>>PDP

Duk Labarai
Shugaban marasa Rinjaye na majalisar Dattijai Abba Moro ya bayyana cewa, Tsohon gwamnan jihar Delta, Ifeanyi Okowa da ya koma APC ne silar faduwar PDP zaben shugaban kasa a 2023. Yace Okowa ko jiharsa bai ci ba, inda yace da wani aka dauko daga kudu ba Okowa ba da za'a iya samun Nasara. Ya fadi wannan maganane a matsayin ga Ifeanyi Okowa da yace yayi dana sanin yin takarar neman shugabancin kasa da Atiku. Moro yace Ifeanyi Okowa idi rufe ya je PDP yana neman a bashi takarar mataimakin shugaban kasa inda yace babu wanda ya tursasashi.
Gyaran matatar man fetur din Fatakwal, Warri da Kaduna yaudarace ba gyaran ake ba>>Inji Masana

Gyaran matatar man fetur din Fatakwal, Warri da Kaduna yaudarace ba gyaran ake ba>>Inji Masana

Duk Labarai
Wani masani a fannin makamashi kuma me sharhi akan al'amuran yau da kullun, Kelvin Emmanuel ya bayyana cewa gyaran matatun man fetur din Najeriya, Fatakwal, Warri da Kaduna duk yaudarace. Ya bayyana hakane a hirar da aka yi dashi a channels TV. Hakan na zuwane yayin da sabbin rahotanni ke cewa matatar man Warri da aka ce ta dawo aiki, wata daya ta yi tana aiki ta tsayawa tun watan Janairu da ya gabata. Matsalar rashin aikin mamatun man fetur din Najeriya matsala ce da ta dade ana fama da ita wadda gwamnatoci da yawa suka kasa shawo kanta.
Hukumar kula da sararin samaniya ta Najeriya ta yi hasashen samun Gajimare da tsawa a fadin kasar

Hukumar kula da sararin samaniya ta Najeriya ta yi hasashen samun Gajimare da tsawa a fadin kasar

Duk Labarai
Hukumar sararin samaniya ta Najeriya, (NiMet) ta yi hasashen samun Gajimare da rana a wasu sassan Najeriya daga ranar Laraba har zuwa Juma'a. A sanarwar data fitar ranar Talata a Abuja, Hukumar tace za'a samu rana a jihohin Arewa daga ranar Laraba zuwa Juma'a. Tace amma za'a iya samun hadari a sararin samaniyar jihohin Kaduna, Adamawa, Sokoto, Kebbi, Zamfara da Taraba da kuma tsawa. Hakanan tace a jihohin Benue, Plateau, Niger, Kwara da Kogi ma abinda ake tsammanin zai faru kenan. A jihohin Delta, Cross River, Akwa Ibom, Rivers da Bayelsa kuma sun ce za'a samu hasken rana da safe inda suma ana tsammanin Hadari da tsawa. A jihohin Kebbi, Taraba, Borno da Adamawa kuwa hukumar tace za'a tashi ranar Alhamisbda tsawa.