Saturday, March 14
Shadow

Duk Labarai

El-Rufai, Amaechi,Buhari, da Osinbajo basu je taron masu ruwa da tsaki na APC ba

El-Rufai, Amaechi,Buhari, da Osinbajo basu je taron masu ruwa da tsaki na APC ba

Duk Labarai
An yi babban taron masu ruwa da tsaki na Jam'iyyar APC a babban birnin tarayya, Abuja ranar Laraba. An yi taronne a hedikwatar Jam'iyyar dake Abuja wanda shine irinsa na farko tun bayan da shugaban kasa, Bola Ahmad ya hau mulki. An saka jami'an tsaro sosai a wajan taron kuma masu ruwa da tsaki na Jam'iyyar da yawa sun halarci taron. Manyan Mutanen da suka halarci wajan taron sun hada da Abdulaziz Yari, Atiku Bagudu, Benjamin Kalu.  Hakanan Gwamnonin jihohin Edo, Benue, Ondo, Ekiti, Kaduna, Jigawa, Nasarawa, Yobe, Niger, Lagos, Kogi, Ogun, da Imo da kuma mataimakin gwamnan jihar Ebonyi duk sun halarci taron. Hakanan tsaffin Gwamnonin jihohin Kogi, Kebbi, Niger, Zamfara, da Plateau duk sun halarci wajan taron. Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu, da Mataimakinsa Kashim Shattim...
Da Duminsa: ‘Yan Bìndìgà sun tare ‘yansandan Najeriya sun kashe 2 daga ciki

Da Duminsa: ‘Yan Bìndìgà sun tare ‘yansandan Najeriya sun kashe 2 daga ciki

Duk Labarai
Tawagar 'yansandan Najeriya da suka fita aiki a karamar hukumar Jos dake jihar Filato sun gamu da kwantan baunar 'yan Bindiga inda suka afka musu suka kashe 'yansanda 2. Lamarin ya farune akan titin Little Rayfield Road da misalin karfe 7:30 pm. Ana zargin dai ko 'yan Fashi ko masu garkuwa da mutanene suka afkawa 'yansandan. 'yansandan da aka kashe sune Inspector Fatoye Femi da Inspector Dafur Dashit. An kama daya daga cikin maharan me suna Auwal Ali.
Duk da yake nasan cewa tsare-tsaren gwamnatina sun jefa ‘yan Najeriya cikin Mawuyacin hali amma kasar ba zata dore ba da an ci gaba da biyan tallafin man fetur>>Tinubu

Duk da yake nasan cewa tsare-tsaren gwamnatina sun jefa ‘yan Najeriya cikin Mawuyacin hali amma kasar ba zata dore ba da an ci gaba da biyan tallafin man fetur>>Tinubu

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayyana cewa, Najeriya ba zata dore ba da an ci gaba da biyan tallafin man fetur. ya bayyana hakane a wajan taron masu ruwa da tsaki na Jam'iyyar APC da ya gudana a Fadarsa dake babban birnin tarayya Abuja ranar Talata. Shugaban ya bayyana cewa, dolene tasa ya cire tallafin man fetur din amma kuma kowace jiha na samun kudi nunki uku fiye da yanda take samu kamin ya hau mulki. Shugaban ya fadi wannan maganane a yayin da bayan cire tallafin man fetur din mutanen Najeriya da yawa suka shiga cikin halin kaka nikayi.
Masu Gàrkùwà da mutane sun sace dalibai 2 a kofar makarantarsu

Masu Gàrkùwà da mutane sun sace dalibai 2 a kofar makarantarsu

Duk Labarai
Rahotanni daga Makurdi Jihar Benue na cewa masu garkuwa da mutane sun sace dalibai biyu daga jami'ar Joseph Sarwuan Tarka University dake jihar. An yi garkuwa da dalibanne a daren ranar Talata a gaban makarantarsu. A hirar da aka yi da daya daga cikin daliban me suna Ashar Lubem ya bayyana cewa dalibai 4 ne aka yi garkuwa dasu kuma lamarin ya jefa daliban makarantar cikin rudani. Kakakin 'yansandan jihar, Sewuese Anene ta tabbatar da faruwar lamarin saidai tace dalibai 2 ne kadai aka yi garkuwa dasu kamar yanda suka samu bayanai. tace kuma suna kan binciken lamarin.
An yi Gàrkùwà da mutane da yawa a kusa da Barikin Sojoji a Abuja

An yi Gàrkùwà da mutane da yawa a kusa da Barikin Sojoji a Abuja

Duk Labarai
Rahotanni daga babban birnin Tarayya Abuja na cewa, masu garkuwa da mutane sun sace mutane da yawa a kusa da barikin sojoji ta Abacha Barracks dake Guzape. Lamarin ya farune da daren ranar Talata. Lamarin ya farune da misalin karfe 11:31pm kuma ya saka tsoro a zukatan mutane Mazauna Abuja. Hakan na zuwane biyo bayan garkuwa da mutane data faru a unguwannin Bwari, Kuje, da Gwagwalada wanda cikin wadanda aka yi garkuwar dasu hadda kananan yara da mata. Hukumar 'yansandan Birnin na Abuja sun tabbatar da faruwar lamarin inda suka ce sun kai dauki wajan da lamarin ya faru kuma sun gano motoci biyu wanda ake tsammanin mutanen ciki ne aka yi garkuwa dasu. Ciki hadda Hon. Shagala Samuel. 'Yansandan sunce sun bincike dazukan dake kusa da inda aka yi garkuwa da mutanen amma basu ga wa...
Matar data fi kowace mace kudi a Najeriya da Afrika, Folorunso Alakija ta makance

Matar data fi kowace mace kudi a Najeriya da Afrika, Folorunso Alakija ta makance

Duk Labarai
Matar da tafi kowace mace kudi a Najeriya da Afrika, Folorunso Alakija ta makance kwata-kwata inda ta daina gani gaba daya. Rahoton hakan ya fito ne daga kafar Sahara Reporters inda suka ce ta samu wannan matsalane dalilin hawan jini. Lamarin ya farane a yayin da suke tafiya tare da mijinta a cikin jirgi inda jirgin ya so samun tangarda. Daga nan ne dai sai ta fara ganin hazo-hazo, wasu na kusa da ita sun bayyana cewa bata dauki wani matakin neman magani da muhimmanci ba kan lamarin wanda hakanne yasa ta kai ga makancewa gaba daya.
Kalli Hotunan Gawurtaccen me Gàrkùwà da mutane da jami’an tsaro suka kama

Kalli Hotunan Gawurtaccen me Gàrkùwà da mutane da jami’an tsaro suka kama

Duk Labarai
Jami'an tsaro sun kama masu garkuwa da mutane dan karbar kudin Fansa su biyu a Barkin Ladi dake Jihar Plateau. Rahoton yace an kama su ne bayan da wasu da aka kama a baya suka bayar da bayanai akan maboyarsu. Kuma an kamasu ne a kauyen Lugere Sho. Hakanan an kara kama wani me garkuwa da mutanen a Kauyen Kwok duk dai a Barkin Ladi kuma yana bayar da bayanai game da ta'asar da yayi a baya ciki hadda garkuwa da mutane a jiharta Filato da Nasarawa. Hakanan ya bayar da bayanai akan wadanda suke aiki tare da maboyarsu inda jami'an tsaro tuni suka bazama dan nemosu.
Gwamnatin Shugaba Tinubu na shirin karbi bashi har sau shidda daga bankin Duniya a wannan shekarar

Gwamnatin Shugaba Tinubu na shirin karbi bashi har sau shidda daga bankin Duniya a wannan shekarar

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Gwamnatin Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu na shirin karbo bashi har sau shidda daga bankin Duniya da jimullar kudin suka kai Dala Biliyan $2.23 a wannan shekarar da muke ciki ta 2025. Bayanai daga bankin Duniyar ya nuna cewa hakan zai kawo yawan kudaden da Bankin ya baiwa Najeriya bashi zuwa jimullar Dala Biliyan $9.25 a cikin shekaru 3 da suka gabata. Hakan na kara nuni da yanda Najeriya ke dogaro da bashi wajan gudanar da ayyukan Gwammati. Rahotanni sun bayyana cewa, a mulkin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu an samu karin yawan bashin da ake bin Najeriya, wanda ko da a shekarar data gabata, shugaban ya ciwo bashi sosai. Hakan na zuwane duk da kiran da shugaban Kungiyar Kwadago ta NLC, Joe Ajaero yayi ga bankin Duniyar na cewa su daina baiwa shuwag...
Hotunan dan shekaru 60 daya nemi auren ‘yar shekaru sha shida sun dauki hankula, wasu dai sun ce kudi gareshi shiyasa

Hotunan dan shekaru 60 daya nemi auren ‘yar shekaru sha shida sun dauki hankula, wasu dai sun ce kudi gareshi shiyasa

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Wani mutum dan shekaru 60 da wata da aka bayyanata a matsayin 'yar shekaru 16 sun bayyana a kafafen sada zumunta suna soyayya. An ga yanda mutumin ya saka mata zobe a hannu yana nunawa alamar ta amince da soyayyarsa. Lamarin dai ya jawo cece-kuce, musamman kasancewarsu kirista inda da dama ke cewa da musulmai ne da ba karamin zagi zasu sha ba.
Ana rade-radin Budurwar Jude Bellingham Kàrùwàcè, gashi kuma har magana ta yi nisa tsakaninsu ya kaita ta gaishe da iyayensa

Ana rade-radin Budurwar Jude Bellingham Kàrùwàcè, gashi kuma har magana ta yi nisa tsakaninsu ya kaita ta gaishe da iyayensa

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Rahotanni sun bayyana cewa Budurwar tauraron dan Kwallon Real Madrid Jude Bellingham watau Ashlyn Castro Karuwace. Dalili kuwa shine an ga ta bude shafi a dandalin yanar gizo na Karuwai a kasar Ingila. Hakanan ana zargin Ashlyn da cewa ta yi karyar Shekaru. Bayanan da ake dasu shine, an haifi Ashlyn a December 17, 1997 a Long Beach dake California wanda a watan Janairu da ya gabata ta cika shekaru 27 kenan. Saidai wata Majiya ta bayyana cewa asalin Shekarun Ashlyn 32 ne. ...