Friday, July 17
Shadow

Da Duminsa: ‘Yan Bìndìgà sun tare ‘yansandan Najeriya sun kashe 2 daga ciki

Tawagar ‘yansandan Najeriya da suka fita aiki a karamar hukumar Jos dake jihar Filato sun gamu da kwantan baunar ‘yan Bindiga inda suka afka musu suka kashe ‘yansanda 2.

Lamarin ya farune akan titin Little Rayfield Road da misalin karfe 7:30 pm.

Ana zargin dai ko ‘yan Fashi ko masu garkuwa da mutanene suka afkawa ‘yansandan.

‘yansandan da aka kashe sune Inspector Fatoye Femi da Inspector Dafur Dashit.

An kama daya daga cikin maharan me suna Auwal Ali.

Karanta Wannan  Kalli Yanda aka gano wani Kirista da yayi amfani da hoton makabartar Musulmai da cewa Kiristane da aka Shyekye dan ya jawo hankalin kasar Amurka

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *