Saturday, February 21
Shadow

Duk Labarai

Da Duminsa: Kamfanin Wutar Lantarki sun janye yajin aikin da suke a Kaduna, Sokoto, Zamfara da Kebbi

Da Duminsa: Kamfanin Wutar Lantarki sun janye yajin aikin da suke a Kaduna, Sokoto, Zamfara da Kebbi

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, kamfanin wutar lantarkin dake kula da wutar lantarki ta Kaduna, Zamfara, Kebbi da Sokoto dake yajin aiki sun janye yajin aikin nasu da ya kwashe kwanaki biyar suna yi. Ma'aikatan kamfanin wutar sun janye yajin aikinne bayan da gwamnan jihar Kaduna, Malam Uba Sani ya shiga tsakani. Gwamnan ya bayyana hakane a shafinsa na sada zumunta inda ya tabbatar da cewa, an janye yajin aikin.
Komai ya tafi daidai a Gwamnatina>>Tsohon Shugaban kasa Buhari ya bugi kirji

Komai ya tafi daidai a Gwamnatina>>Tsohon Shugaban kasa Buhari ya bugi kirji

Duk Labarai
Tsohon Shugaban kasa, Muhammad Buhari ya bayyana cewa a zamanin mulkinsa abubuwa sun tafi yanda ya kamata. Ya bayyana hakane a gawarsa da wasu 'yan jarida da suka kai masa ziyara a Daura. Yace abubuwan ci gaba da ya kawo a zamanin mulkinsa za'a dade ana amfana dasu a Najeriya. Shugaban ya bayyana cewa, a shekarar 2015 da ya karbi mulki, ya gaji matsaloli da yawa daga gwamnatin Jam'iyyar APC wanda suka hada dana rashin tsaro, matsalar tattalin arziki da sauransu.
Amurkawa na zuwa Asibitocin Najeriya neman magani>>Inji Gwammatin Tarayya

Amurkawa na zuwa Asibitocin Najeriya neman magani>>Inji Gwammatin Tarayya

Duk Labarai
Mataimakin Shugaban kasa, Kashim Shettima ya bayyana cewa, an samu ci gaba sosai a Najeriya musamman ta fannin lafiya inda yace 'yan kasar Amurka na zuwa Najeriya neman magani. Ya bayyana hakane a yayin ganawa da wata kungiyar Likitocin da suka kai masa ziyara a Abuja fadar shugaban kasa. Yace kwanannan wasu marasa lafiya daga kasar Amurka su 13 suka zo Asibitin Zenith Medical and Kidney Centre aka musu dashen koda kuma an samu nasarar yin aikin. Yace kuma sun samu aikin a farashi me sauki kasa da yanda ake yinsa a kasar ta Amurka. Mataimakin shugaban kasar ya kuma jinjinawa shugaban Asibitin me suna Dr. Olalekan Olatise inda yace gwarzo ne wajan kula da lafiya. Saidai ya koka game da yanda 'yan Najeriya da yawa ke fama wajan aikin Koda saboda tsadarsa inda yace wasu na dog...
Yajin aiki akan kara kudin kiran waya ba gudu ba gudu ba ja da baya>>TUC

Yajin aiki akan kara kudin kiran waya ba gudu ba gudu ba ja da baya>>TUC

Duk Labarai
Kungiyar kwadago ta TUC ta jadada cewa, babu gudu ba ja da baya akan maganar yajin aikin da take shirin yi dan nuna rashin jin dadin karin kudin kiran waya dana data. Shugaban kungiyar, Festus Osifo ne ya bayyana haka a ganawar da aka yi dashi a ChannelsTV. Yace abinda ya kawo tsadar kudin gudanarwa na kamfanonin sadarwar, farashin canjin kudin Naira da dala ne wanda kuma gwamnati zata iya yin maganinsu. Yace gwamnati ce ke da alhakin magance matsalar ta kamfanonin sadarwar ba wai su rika fanshewa akan talakawa ba.
Kalli Bidiyo: ‘Yan Uwan me yada badala a Tiktok, Yahya Amerika sun taru sun masa dukan kawo wuka saboda zubar musu da mutunci da yake inda yace ya tuba ba zai kara ba

Kalli Bidiyo: ‘Yan Uwan me yada badala a Tiktok, Yahya Amerika sun taru sun masa dukan kawo wuka saboda zubar musu da mutunci da yake inda yace ya tuba ba zai kara ba

Duk Labarai
ABIN KOYI: 'Yan Uwan Wani Mai Yada Baďàla A Țiķțok me suna Yahya Amerika Sun Taŕu Sùm Yi Mašà Ďuķan Țšiýa Saboda Yadda Yake Źùbaŕwa Da Dañginsu Mùtùnci Bayan ya daku, mutumin ya ce daga yau ya tuba ba zai sake ba, kuma zai goge shafin nasa na țiķtoķ. https://www.tiktok.com/@babyn.babybackup4/video/7468258337616907526?_t=ZM-8ti5YVGGBwk&_r=1 Hutudole ya fahimci cewa, yakan rika bayyanawa a shafinsa cewa duk macen da take son a yi lalata da ita, ta mai magana. Fatan mu shine Allah yasa da gasken ya daina.
Kalli Bidiyon yanda dansandan Najeriya ya dirkawa jami’in kula da hanya Roaf Safety Harsashi saboda rikicin lambar mota

Kalli Bidiyon yanda dansandan Najeriya ya dirkawa jami’in kula da hanya Roaf Safety Harsashi saboda rikicin lambar mota

Duk Labarai
Rahotanni daga jihar Legas na cewa, wani dansanda ya dirkawa jami'in kula da hanya, wanda aka fi sani da Road Safety harsashi a ciki biyo bayan rikicin lambar mota. https://twitter.com/ChuksEricE/status/1887475766398435395?t=6Jp120yRIhks9cEmvusgug&s=19 kalli bidiyon anan Tuni dai aka garzaya da jami'in na FRSC zuwa Asibiti inda shi kuma dansandan aka kamashi.
Kallo Hotuna yanda aka gano gawar wani dan siyasa har ta fara rubewa bayan an yi gàrkùwà dashi

Kallo Hotuna yanda aka gano gawar wani dan siyasa har ta fara rubewa bayan an yi gàrkùwà dashi

Duk Labarai
Masu garkuwa da mutane a ranar 24 ga watan Disamba daya gabata na shekarar 2024 sun yi garkuwa da dan siyasa na jihar Anambra me suna Hon Justice Azuka. Sun yi garkuwar dashine a garin Onitsha bayan nuna masa bakin Bindiga. 'Yansanda sun yi nasarar kama wadanda ake zargi da wannan aika-aika inda suka amsa laifinsu. A ranar 6 ga watan Fabrairu na shekarar 2025 ne wanda ake zargin suka kai 'yansanda gadar Second Niger Bridge inda suka ce anan ne bayan sun kashe Hon Justice Azuka suka jefar da gawarsa. Hadin gwiwar jami'an tsaro yayi nasarar gano gawar dan siyasar wadda har ta fara rubewa. Justice Azuka dan Jam'iyyar Labour party ne kuma yayi nasarar kwace kujerar majalisar tarayya ne daga hannun dan takarar Jam'iyyar PDP Hon. Douglas Egbuna a kotu shekara daya kamin faruw...
YANZU YANZU: An Binciko yadda Nuhu Ribaɗu yayi Awun gaba da wasu Biliyoyin kuɗaɗe a lokacin da yake shugaban Hukumar EFCC, inji Fitaccen mai Binciken nan Dr. Idris

YANZU YANZU: An Binciko yadda Nuhu Ribaɗu yayi Awun gaba da wasu Biliyoyin kuɗaɗe a lokacin da yake shugaban Hukumar EFCC, inji Fitaccen mai Binciken nan Dr. Idris

Duk Labarai
Nasan wanda yake Sauyawa Nuhu Ribaɗu Dalar Amurka na cin hanci da rashawa. Fitaccen mai bincike kuma mai fafutukar kare haƙƙin bil'adama a ɗan asalin Najeriya, mazaunin kasar Ingila, Dr. Idris Ahmed ya bayyana wasu muhimman zarge-zarge da ya sani akan Malam Nuhu Ribadu mai taimakawa Shugaban kasa kan sha'anin tsaron Najeriya. Dr. Idris ya bayyana cewa, “A lokacin da yake shugaban hukumar EFCC, ya karbi makudan kudaden cin hanci. Musammab dalar Amurka, akwai wani wanda Shi ne me yiwa Nuhu Ribadu canjin dalar Amurka, wanda tsohon dan sanda, ne ACP mai ritaya ne ana kiransa da suna (retired) Rabiu Abubakar Shariff. Rabiu Abubakar Shariff shi clasmate dina ne lokacin muna karatun sakandare. Shine wadda Lieutenant General Tukur Buratai ya turo shi zuwa kasar Burtaniya, domin ya saci sa...
YANZU YANZU: Sabida tsohon Allah da nake dashi a lokacin Mulkina Ko Fentin Gidana Ban Canja Ba A Tsawon Shekaru Takwas Da Na Yi Akan Mulki, Cewar Buhari

YANZU YANZU: Sabida tsohon Allah da nake dashi a lokacin Mulkina Ko Fentin Gidana Ban Canja Ba A Tsawon Shekaru Takwas Da Na Yi Akan Mulki, Cewar Buhari

Duk Labarai
Tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari ya bayyana cewa a tsawon mulkin da ya yi shekara takwas, ko sake fentin gida bai yi ba . Buhari ya faɗi haka ne a lokacin da ƙungiyar ƴan jarida reshen kafofin yaɗa labarai a Katsina suka kai masa ziyara a gidansa dake garin Daura. Ya ce yana cikin ƙoshin lafiya idan aka kwatanta shi da abokansa da suka taso tun suna yara, inda wasu daga cikinsu da sanda suke dogarawa su yi tafiya. Ya kuma ce Mataimakin Shugaban ƙasa, kashin Shattima ne ya fidda kuɗi daga aljihunsa ya ke gyara masa gidansa na Kaduna. “Da zarar an kammala gyaran gidan zan koma kaduna”, inji Buhari. Tunda da farko, shugaban tawagar ƴan jaridun, Yusuf Ibrahim Jargaba ya faɗa wa tsohon shugaban ƙasar cewa sun kawo masa ziyarar ban girma ne da kuma yi masa ban gajiya. Jar...
DA DUMI DUMINSA; Za’a ƙirƙiri Sabbin Jahohi guda 31, Mun samu bukatar ƙirƙiro sabbin Jihohi 31 a Najeriya – Kalu

DA DUMI DUMINSA; Za’a ƙirƙiri Sabbin Jahohi guda 31, Mun samu bukatar ƙirƙiro sabbin Jihohi 31 a Najeriya – Kalu

Duk Labarai
Kwamitin gyaran kundin tsarin mulki na Majalisar wakilan Najeriya, ya ce ya karbi buƙatar ƙirƙiro jihohi 31 daga sasan kasar, domin ƙara yawan jihohin da ake da su akan 36 dake wanzuwa yanzu haka. Shugaban kwamitin Benjamin Kalu, wanda shi ne mataimakin shugaban Majalisar wakilai, ya bayyana haka a zaman majalisar.Kalu ya ce bukatun sun hada da 6 daga Arewa ta Tsakiya, 4 daga Arewa ta Gabas, 5 daga Arewa ta Yamma, sai kuma 5 daga Kudu maso Gabas da 4 daga Yankin Kudu maso Kudu da 7 daga Kudu maso Yamma.Ga jerin bukatun kamar yadda Kalu ya bayyana. Jihar Okun daga Kogi Jihar Okura daga Kogi Jihar Confluence daga Kogi Jihar Benue Ala daga Benue Jihar Apa daga Benue Jihar FCT daga FCT Jihar Amana daga Adamawa Jihar Katagum daga Bauchi Jihar Savannah daga Borno J...