Wednesday, March 11
Shadow

Duk Labarai

Ana barazanar kkasheni saboda na yi magana akan Peter Obi>>Inji Me magana da yawun APC, Felix Morka

Ana barazanar kkasheni saboda na yi magana akan Peter Obi>>Inji Me magana da yawun APC, Felix Morka

Duk Labarai
Me magana da yawun Jam'iyyar APC, Felix Morka ya bayyana cewa, an aika masa barazanar kisa har guda 400 wanda daga ciki guda 200 kai tsaye aka ce za'a kasheshi ko yankashi saboda yayi magana akan Peter Obi. Ya bayyana hakane a hirar da aka yi dashi a gidan talabijin na AriseTV inda yace an masa kazafin cewa ya yiwa rayuwar Peter Obi Barazana. Yace shi karya ake masa, babu inda yawa rayuwar Peter Obi Barazana. Yace tuni aka fara kaiwa wasu daga cikin 'yan uwansa hari inda yace ya dauki bayanai akan wannan barazana da ake masa inda zai kaiwa hukumar 'yansanda korafi. A baya dai, Shima Peter Obi yace ana yiwa rayuwarsa barazana.
Sabon Shugaban Hukumar Kula Da Gidan Yari Na Jihar Katsina Ya Ziyarci Buhari Bayan Ya Karbi Ragamar Kama Aiki

Sabon Shugaban Hukumar Kula Da Gidan Yari Na Jihar Katsina Ya Ziyarci Buhari Bayan Ya Karbi Ragamar Kama Aiki

Duk Labarai
Daga Comr Nura Siniya Tsohon shugaban kasar Nijeriya Muhammad Buhari, ya karɓi baƙuncin sabon shugaban ma'aikatan hukumar kula da gidan gyaran hali na jihar Katsina Mr. Umar Baba, a gidansa na Daura dake jihar Katsina Sabon Kwantirolan NIS Umar Baba, ya ziyarci Muhammadu Buhari a gidansa da ke Daura, a ranar 7 ga Janairu, 2025.
Farashin kayan Abinci zai yi tashin gwauron zabi saboda manoman Arewa sun zabi kai kayan amfanin gonarsu kasashen waje

Farashin kayan Abinci zai yi tashin gwauron zabi saboda manoman Arewa sun zabi kai kayan amfanin gonarsu kasashen waje

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa ana hasashen farashin kayan abinci zai yi tashin gwauron zabi saboda manoma a Arewa sun zabin kai kayan abincinsu kasashen waje su sayar maimakon sayarwa a gida Najeriya. Manoma a jihohin Kaduna da Kwara sun koka da rashin amfanin gona me kyau saboda karancin ruwan sama da krkatar da kayan noman da 'yan siyasa suka yi. Saidai manoma a jihohin Jigawa, Kano da Yobe sun bayyana samun amfanin noma sosai irinsu Dawa, Wake, Masara, Gero da Sauransu. Saidai sun bayyana cewa, mafi yawancin kayan amfanin nasu zasu kaisu jihohin wajene dan sayarwa. Hakan a binciken jaridar Punchng ya nuna cewa, zai iya kaiwa ga hauhawar farashin kayan abinci a wannan shekarar.
Shugaba Tinubu ya canja ra’ayi kan maganar sauya Fasalin Haraji

Shugaba Tinubu ya canja ra’ayi kan maganar sauya Fasalin Haraji

Duk Labarai
Babban me baiwa shugaban kasa shawara kan harkar sadarwa, Daniel Bwala ya bayyana cewa, shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu zai iya la'akari da wasu sharuda daga gwamnoni akan maganar canja fasalin harajin kasa. Kudirin dokar canja karba da raba harajin wanda ke gaban majalisar tarayya ta fuskanci koma bayan da rashin karbuwa musamman ga gwamnonin Arewa inda hakan yasa dole majalisar ta dakatar da zartar dashi inda a yanzu ake bi dan jin ra"ayin jama'a. Duk da sukar da wannan kudirin canja haraji ke fuskanta, shugaba Bola Ahmad Tinubu ya jajirce akan cewa babu gudu ba ja da baya kan lamarin. Bwala a yayin hira da gidan talabijin na ChannelsTV ya bayyana cewa, maganar kudirin dokar canja fasalin haraji babu gudu ba ja da baya kuma majalisa zata amince da kudirin. Yace abinda gwamno...
Hotuna: Yadda dan gidan ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya kammala digiri na biyu a Jami’ar kasar Ingila, Inda ya karanci fannin shari’a. Ministan ne ya wallafa hakan a shafinsa na X, inda yake alfahari da hakan

Hotuna: Yadda dan gidan ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya kammala digiri na biyu a Jami’ar kasar Ingila, Inda ya karanci fannin shari’a. Ministan ne ya wallafa hakan a shafinsa na X, inda yake alfahari da hakan

Duk Labarai
Yadda dan gidan ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya kammala digiri na biyu a Jami'ar kasar Ingila, Inda ya karanci fannin shari'a. Ministan ne ya wallafa hakan a shafinsa na X, inda yake alfahari da hakan. Nyesom Wike
An saki Mubarak Bala, ɗan Najeriyar nan da ya yi suna wajen sukar addini bayan shafe shekara huɗu tsare a gidan yari kan tuhume-tuhumen da suka shafi ɓatanci ga addini

An saki Mubarak Bala, ɗan Najeriyar nan da ya yi suna wajen sukar addini bayan shafe shekara huɗu tsare a gidan yari kan tuhume-tuhumen da suka shafi ɓatanci ga addini

Duk Labarai
Ya shaida wa BBC irin ƙalubalen da masu aƙida irin tasa ta rashin yadda da kowane addini ke fuskanta. Mubarak Bala, shugaban kungiyar Humanist Association of Nigeria kuma fitaccen mai ikirarin rashin addini, ya samu 'yanci bayan shafe shekaru huɗu a gidan yari kan zargin batanci. An yanke masa hukuncin shekara 24 a kurkuku tun a fari a shekarar 2022, bayan ya amsa laifuka 18 da suka haɗa da batanci, tayar da zaune tsaye, da cin zarafin addini ta kafar sada zumunta. Hukuncin ya samo asali ne daga wallafa ra'ayoyinsa na sukar addinin Islama, Allah, da Annabi Muhammad (SAW) ta kafar sada zumunta, wanda ya haifar da fushin al'umma. Kafin a yanke masa hukunci, Mubarak ya yi shekara biyu yana jiran shari’a a tsare tun bayan kamashi a Kaduna a ranar 28 ga Afrilu, 2020. A cewar rahoton BB...
Adawa tsakanin tsofaffin gwamnoni na mayar da Kano baya – Garo

Adawa tsakanin tsofaffin gwamnoni na mayar da Kano baya – Garo

Duk Labarai
Tsohon ɗantakarar mataimakin gwamnan jihar Kano a zaɓen 2023, Murtala Sule Garo ya ce adawar siyasar da ke tsakanin tsofaffin gwamnoni na hana jihar ci gaba. Garo ya kuma yi kira ga jagororin siyasar jihar su mayar da kubensu, tare da haɗa ƙarfi da ƙarfe domin ciyar da jiharsu gaba. Garo ya bayyana haka ne a wani faifan bidiyo da jaridar Daily Trust ta ruwaito, inda ya ce, "babu daɗi ganin jihohi irin Zamfara da ba ta kai Kano ba, tsofaffin gwamnoninta suna ajiye bambancin siyasa suna haɗuwa domin ciyar da jihar gaba. Mu a nan Kano, da wahala ka samu tsofaffin gwamnoni sun haɗu domin tattauna hanyoyin da za a magance matsalolin jihar." "Ina kira ga tsofaffin gwamnoninmu, idan har da gaske suna ƙaunar Kano, su haɗa kai. Ba a samun ci gaba da rabuwar kai. Dole jagororin si...
Yarinyar da ake tuhuma da zuba wa miijinta guba a abinci a Jigawa ta amsa laifinta

Yarinyar da ake tuhuma da zuba wa miijinta guba a abinci a Jigawa ta amsa laifinta

Duk Labarai
Yarinyar nan mai shekara 14 da ƴansanda suka tuhuma da kashe abokin mijinta bayan zuba musu guba a abinci a jihar Jigawa ta amsa laifinta a gaban alƙali Al'amarin dai ya faru ne a ranar Lahadin 15 ga watan Disambar 2024 a ƙauyen Bakata da ke ƙaramar hukumar Kiyawan jihar Jigawa. Yarinyar dai ta saka wa mijinta da abokansa guba a taliya, kuma nan da nan suka fita daga hayyacinsu, inda aka kai su asibitin garin Jahun inda a nan ne ɗaya daga cikin abokan mijin ya mutu. Yarinyar ta amsa laifin saka gubar, sai dai kuma ta ce tsohon saurayinta wanda ɗanuwanta ne ya ba ta gubar domin ta saka wa mijin nata da abokansa a abinci. Sai dai tsohon saurayin ya ce ba ya garin lokacin da yarinyar ta je garin. Yanzu haka yarinyar tana tsare a hannun ƴansanda inda shi kuma saurayin ke tsare a gi...
Najeriya ta naɗa Éric Chelle a matsayin kocin Super Eagles

Najeriya ta naɗa Éric Chelle a matsayin kocin Super Eagles

Duk Labarai
Hukumar ƙwallon ƙafa ta Najeriya NFF ta naɗa tsohon kocin tawagar Mali, Éric Chelle, a matsayin kocin tawagar ƙwallon ƙafa ta Super Eagles. Chelle mai shekara 47 ya jagoranci Mali har zuwa zagayen kwata fayinal a gasar Kofin Ƙasashen Afirka ta 2023 a Ivory Coast, kafin mai masaukin baƙi ta doke su. NFF ta ce ta amince da naɗin nasa ne bayan kwamatinta na musamman ya bayar da shawarar yin hakan a yau Talata. Naɗin nasa na zuwa ne bayan NFF ta kasa daidaitawa da Bruno Labbadia ɗan ƙasar Jamus game da batun biyan haraji bayan sanar da ba shi aikin a watan Agustan 2024. Kafin naɗin nasa, shugaban NFF Ibrahim Musa Gusa ya faɗa wa manema labarai cewa sabon kocin da za su bai wa aikin shi ne zai jagoranci tawagar Super Eagles ta 'yanwasan cikin gida zuwa gasar kofin Afirka ta CHAN - w...
Kwanaki kadan bayan da ya karyata labarin komawa PDP, An hangi tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai a ofishin Jam’iyyar SDP

Kwanaki kadan bayan da ya karyata labarin komawa PDP, An hangi tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai a ofishin Jam’iyyar SDP

Duk Labarai
Tsohon gwamman jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya saka mutane rudani bayan da aka ganshi a hedikwatar Jam'iyyar SDP a ranar Talata. Hakan na zuwane kwanki biyu bayan da Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya karyata labaran da suka ce ya bar Jam'iyyar APC zuwa PDP. Tsohon shugaban NIMASA, Ahmad Tijjani Ramalan ne ya wallafa hotunan zuwan El-Rufai ofishin SDP. Ya bayyana cewa an yi zama tsakanin El-Rufai da SDP ne a kokarin da ake na yin hadaka dan samo hanyar yin nasara akan Jam'iyyar APC a zaben shekarar 2027.