Sanata Dino Melaye ya ziyarci gidan wani abokinsa inda yaci karo da damisa.
Sanata Melaye ya bayyana mamakin abin saidai an gaya masa basa cutarwa.
https://www.youtube.com/watch?v=8PCMEVIwSRY
Ya saka bidiyon a shafinsa na sada zumunta inda yake bayyana mamakinsa.
Rahotanni na cewa an samu mutuwar mutane da dama sakamakon tsananin zafi a Indiya. Hukumomin jihohin gabashin ƙasar, Odisha da Bihar sun ce mutane 15 ne suka rasu a ranar Alhamis, kuma suna ci gaba da bincike kan lamarin.
An haramtawa ma'aikata zirga-zirga a tsakiyar rana.
Ana hasashen cewa za a ci gaba da fuskantar tsananin zafi a gabashi yayin da ake hasashen za a samu sauƙin zafin a Arewa maso Yamma da kuma tsakiyar Indiya.
Gamayyar ƙungiyoyin ƙwadago na TUC da NLC a Najeriya sun yanke shawarar tsunduma yajin aikin sai baba ta gani sakamakon rashin cimma yarjejeniya tsakaninsu da gwamnatin tarayya.
Gamayyar ƙungiyoyin sun sanar da hakan ne da yammacin ranar Juma'a bayan wani taro da suka yi inda suka tattaunawa yiwuwar tsunduma yajin aikin.
A farkon makon nan ne dai manyan ƙungiyoyin ƙwadago guda biyu suka yi watsi da tayin naira 60 da gwamnatin tarayya ta yi masu a matsayin albashi mafi ƙanƙanta, biyo bayan zaman da suka yi da gwamnatin tarayya, inda a nan ne gwamnatin ta yi tayin.
Da farko dai sai da gwamnatin Najeriyar ta fara kara naira dubu uku a kan tayin naira dubu 47 da ta yi a baya.
Su ma ƙungiyoyin ƙwadagon sun rage dubu uku daga naira 497 da suke nema a matsayin albashi mafi ƙanƙanta....
Ɗan takarar shugaban Nijeriya na jam'iyyar NNPP a zaɓen 2023, ya zargi 'yan ƙasar a kan fifita siyasar kuɗi maimaikon zaɓar mutane masu aƙidar da za su iya kawo canji.
Injiniya Rabi'u Musa Kwankwaso ya ce dimokraɗiyyar Najeriya ta samu koma-baya saboda wasu 'yan siyasa da kan sayi ƙuri'un mutane ta hanyar ba su atamfa ko taliya.
A cewarsa, irin wannan tunani na ɗaya daga cikin abubuwan da suka jefa al'ummar ƙasar cikin halin matsin rayuwa da taɓarɓarewar tsaron da hukumomi suka gaza shawo kansu ya zuwa yanzu.
Ya kuma ce rashin iya mulki ne ya haddasa taɓarɓarewar al'amura kamar tsaro da tattalin arziƙi a Najeriya.
Rabi'u Musa Kwankwaso ya bayyana haka a jerin hirarrakin da BBC ta yi da wasu ƙusoshin siyasar Nijeriya a wani ɓangare na cika shekara 25 da mulkin dimokraɗiyya karon...
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayyana cewa, dawo da taken Najeriya na daya daga cikin muhimman abubuwan da yake son yi a mulkinsa.
Ya bayyana hakane a yayin ganawa da kungiyar dattawan Najeriya, ACF.
Tinubun dai ya sakawa dokar data dawo da tsohon taken Najeriya hannu wanda hakan ya jawo cece-kuce inda mutane ke cewa ba wannan ne matsalar kasar ba.
Shugaba Tinubu ya kuma jawo hankali kan samun hadin kai a Najeriya.
Hukumar 'yansandan jihar Legas ta bakin tsohuwar kakakin hukumar, Dolapo Badmus ta bayyana cewa rashin iya taken Najeriya, kwakaki 3 bayan shugaban kasa ya saka shi a matsayin doka babban laifi ne.
Ta bayyana hakane a shafinta na Instagram inda take bayar da misalin wani me makaranta data sa a kama saboda yana rera tsohon taken Najeriyar.
Tace rashin iya taken Najeriyar cin amanar kasa ne.
Ta baiwa mutane shawarar su samu lauyoyi su musu karin bayani.
‘’If, as at today, three days after the President of Federal Republic of Nigeria signed and assented the New National Anthem into law and you are not able to recite it in a whole, then you are a suspect
I just passed through a private school and I could here them singing the old National Anthem! "Arise oh compatriots"! (We are...
Tsohuwar kakakin 'yansandan jihar Legas, Dolapo Badmus ta yi kiran a kama shugaban wata makaranta me zaman kanta da babban malamin makarantaar saboda rera tsohon taken Najeriya.
Ta bayyana cewa, ta zo wucewa ta kusa da makarantar ne sai ta ji suna rera tsohon taken Najeriyar.
Tace tuni ta yiwa 'yansanda magana kan a kamasu tare da gurfanar dasu a gaban kotu dan musu hukunci.
Tace kwanaki 3 bayan da shugaban kasa ya sakawa dokar canja taken Najeriyar hannu, duk wanda aka samu bai iyashi ba, to me laifi ne.
Tace kada wanda ya tambayeta laifin me suka yi, duk wanda ke da tambaya, ya samu lauya ya masa karin bayani.
Tace duk wanda bai iya sabon taken Najeriya ba, to yana cin amanar kasane.
‘’If, as at today, three days after the President of Federal Republic of Nigeria sign...
'Yansanda a jihar sokoto sun kama wani mutum saboda siyar da 'ya'yansa 6.
Mutumin ya sayar da jimullar kananan yara 28 ciki hadda 'ya'yan cikinsa 6.
Kwamishinan 'yansandan jihar, CP Ali Hayatu Kaigama ya tabbatar da faruwar lamarin inda yace an kubutar da 21 daga cikin yaran.
Mutumin me suna, Bala Abubakar yana baiwa wasu mata, Kulu Dogon yaro da Elizabeth Ojah yaranne inda su kuma suke bashi Naira dubu dari da hamsin ko kuma Naira dubu dari biyu da hamsin.
Ana cewa wai za'a kaisu Abujane wajan wani mutum da zai rika kula dasu.
Rahotanni sun bayyana cewa, 'yan Boko Haram 3 da iyalansu sun mika wuya inda sukace sun tuba ga sojojin Najeriya.
'Yan Boko Haram din masu sunan Umar Ibn Khatab, Ibn Salih da Abdulrahman sun mika kansu ne ranar 29 ga watan Mayu.
Sun tsere ne daga maboyarsu dake Njimia bayan da sojoji suka bude musu wuta.
Sun kuma mika bindigun AK47 da harsasai da keke.