Tuesday, February 17
Shadow

Duk Labarai

Hoto: Masu Gàŕkùwà da mutane sun kàśhèshi bayan karbar kudin fansa har sau biyu

Hoto: Masu Gàŕkùwà da mutane sun kàśhèshi bayan karbar kudin fansa har sau biyu

Kaduna, Tsaro
Masu garkuwa da mutane sun kashe malami a Makarantar Kaduna Polytechnic, Dr. Levy Makama Pondu bayan da suka yi garkuwa dashi kuma suka karbi kudin fansa har sau biyu. An yi garkuwa dashine ranar August 16, 2024 a yayin da yake komawa gida daga gonarsa bayan ya je ya biya ma'aikatansa. 'Yan uwa da abokan arziki da dalibansa sun hau shafukan safa zumunta inda suke ta bayyana alhinin rashinsa.
Hoto: Karuwa ta kàshè abokin làlàtàrtà bayan da ya dauke ta ya kai gidansa

Hoto: Karuwa ta kàshè abokin làlàtàrtà bayan da ya dauke ta ya kai gidansa

Tsaro
Wata karuwa ta kashe abokin lalatarta bayan da ya dauketa ya kai gidansa. Lamarin ya farune a jihar Legas a unguwar Jakande. Mutumin me suna Okafor ya dauki karuwar, Joy Kelvin ya kai gidansa inda a canne ta caka masa wuka ya mutu. Lamarin ya faru a daren 6 ga watan October inda a wayewar gari watau ranar 7 ga wata sai abokin mamacin ya kira 'yansanda. An garzaya da Okafor zuwa Asibitin Marina inda a canne suka tabbatar ya mutu. Tuni dai aka kama Joy inda shi kuma aka kai gawarsa zuwa mutuware yayin da aka ci gaba da neman 'yan uwansa.
Muna Maraba da Kwankwaso ya zama mataimakin Obi>>Inji Jam’iyyar Labour party

Muna Maraba da Kwankwaso ya zama mataimakin Obi>>Inji Jam’iyyar Labour party

Siyasa
Jam'iyyar Labour party ta yi maraba da maganar da tsohon gwamnan Kano Dr. Rabiu Musa Kwankwaso yayi na cewa zai iya zama mataimakin Obi a zaben 2027. A wata hira ce dai da aka yi Kwankwaso ya bayyana haka inda yace idan an bi tsari me kyau aka cimma yarjejeniya duk da yana sama da Peter Obi a siyasa da shekaru zai iya zama mataimakinsa. Sakataren jam'iyyar Labour Party, Umar Farouk ne ya bayyana haka inda yace amma kada Kwankwaso ya bata rawarsa da tsalle saboda kalaman cewa yafi Peter Obi shahara a siyasa. A baya dai Peter Obi da Kwankwaso sun so hadewa amma lamarin bai yiyu ba, saidai a wannan karin ko lamarin zai tabbata?
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu zai sallami ministoci 11 da sauran manyan ma’aikata

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu zai sallami ministoci 11 da sauran manyan ma’aikata

labaran tinubu ayau
Rahotanni sun bayyana cewa, shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu zai sallami Ministoci 11 daga majalisarsa ta zartaswa. Me baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin yada labarai,Bayo Onanuga ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar. Saidai bai fadi zuwa yaushene Shugaban kasar zai dauki wannan mataki ba. Amma wata majiya a fadar shugaban kasar tace a cikin satin da mukene ake tsammanin za'a fitar da sanarwar garambawul din. Matsin rayuwa na daya daga cikin abinda 'yan Najeriya ke kuka dashi a gwamnatin Bola Ahmad Tinubu wanda ke da alaka da yanayin mulkin da yake gudanarwa.
DA ƊUMI-ƊUMI: Matatar Mai Ta Ɗangote Za Ta Fara Sayar Da Mai Kaitsaye Ga Ƴan Kasuwa

DA ƊUMI-ƊUMI: Matatar Mai Ta Ɗangote Za Ta Fara Sayar Da Mai Kaitsaye Ga Ƴan Kasuwa

Siyasa
Bayan cikar wa'adin yarjejeniyar da suka ƙulla da kamfanin mai na ƙasa NNPC tun da farko, yanzu haka matatar mai ta Ɗangote za ta fara saida mai kaitsaye ga duk wasu ƴan kasuwa masu buƙata. A Rahoton da Jaridar Dokin Ƙarfe TV ta samu, hakan na zaman wani mataki ne na buɗe ƙofa ga kowa da kowa da ke buƙatar sayen man ba wai iya NNPC kawai ba. Kowane ɗan kasuwa da ke buƙatar mai daga yanzu zai iya zuwa matatar man ta Ɗangote kaitsaye su yi ciniki a tsakaninsu. Wannan tsari, zai kuma ba wa kasuwa dama ta yi halinta da kanta batare da an ƙayyade farashi ba, inda matatar za ta saida man kaitsaye ga ƴan kasuwa a farashin da ta ke so ko mai saya yake so.
An kama wata budurwa bayan da saurayi ya kashe mata makudan kudade amma tace ba zata aureshi ba

An kama wata budurwa bayan da saurayi ya kashe mata makudan kudade amma tace ba zata aureshi ba

Duk Labarai
'Yansanda a jihar Legas sun kama wata budurwa me suna Victoria Effiong, inda aka kaita kotu bisa zargin ta cinyewa saurayinta kudi da sauran kaya amma taki yadda ta aureshi. Jimullar kudaden d Victoria ta karba a hannun saurayin nata sun kai Naira miliyan 2.8. Jami'in dansanda dake gabatar da kara a kotun magistre dake Legas, Inspector Chinedu Njoku ya bayyana cewa, budurwar ta kuma samu wayar iphone da kudinta ya kai Naira 240,000 daga wajan saurayin. Sannan ya sai mata agogo da kayan sawa da jaka da takalma da suka kai na Naira 350,000. Sannan ya bata jimullar kudin abinci na naira 868,000. Akwai kuma wata Naira 300,000 data taba cirewa daga asusun ajiyarsa na banki. Lamura sun rinchabene bayan da saurayin nata me suna Dominic Asuquo ya gano tana shirin auren wani can ...
Kalli Bidiyon yanda aka kama wasu ‘yan Luwadi a Najeriya da abinda aka musu

Kalli Bidiyon yanda aka kama wasu ‘yan Luwadi a Najeriya da abinda aka musu

Duk Labarai
Wasu matasa da aka kama da zargin Luwadi an jasu a tsakiyar titi aka kunyatar dasu. Bidiyon faruwar lamarin ya watsu sosai a kafafen sada zumunta inda aka gansu ana dukansu. https://twitter.com/phspecials/status/1842825091660317055?t=C06w-Tzxi8QRi1-xNT2wVA&s=19 Lamarin dai ya jawo cece-kuce inda wasu dake kare lamarin luwadi da Madigo suke kukan cewa bai kamata a dakesu ba.