Saturday, February 14
Shadow

Duk Labarai

Sunaye masu dadi na maza da mata

Duk Labarai
Bari mu fara da sunayen mata: Bilkisu Badiya Basma Balaraba Binta Safara'u Sadiya Sailuba Salamatu Safiya Sakina Siyama Sa'adatu Sahara Rashida Rumasa'u Rabi'atu Ramla Rahanatu Ramatu A'isha Amina Adama Aina'u Asia Faiza Fadila Fauziyya Hauwa Hannatu Hanifa Hablatu Hadiza Jamila Kamila Khadija Khausar Maryam Marfu'a Maimuna Madina Nafisa Nana Nusaiba wasila Zainab Zahara'u Ga kuma Sunayen Maza masu dadi: Aminu Abubakar Ali Ashiru Asiru Abdulrahman Abdullahi Abdulbaqi Abdulhamid Abdulkarim Abdulkadir Bashir Buhari Bala Bukkar Biliya Dahiru Fahad Falalu Faizu Garba Gali Habibu ...
Yanzu-Yanzu:EFCC ta kafa kwamiti dan binciken tsohon gwamnan jihar Kaduna malam Nasiru Ahmad El-Rufai

Yanzu-Yanzu:EFCC ta kafa kwamiti dan binciken tsohon gwamnan jihar Kaduna malam Nasiru Ahmad El-Rufai

Kaduna, Siyasa
Hukumar yaki da rashawa da cin hanci, EFCC ta kafa wani kwamiti na musamman dan binciken zargin da akewa tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai kan satar Naira Biliyan 423. Za'a binciki tsohon gwamnan ne tare da wasu manyan da suka yi aiki tare da shi a gwamnatinsa. Nan gaba kadan ake sa ran EFCC din zasu gayyaci El-Rufai dan binciken sa. Hukumar ta EFCC tace sun karbi korafi dake bukatar a bincike tsohon gwamnan na jihar Kaduna. za a bincike gwamnan ne tare da sauran mukarrabansa da suka yi aiki tare dashi tsakanin shekarau takwas daya yi akan karagar mulki. Cikin wadanda za a bincika hadda ma'aikatan KADRIS KADRA amma banda injiniya Amina jafar Ladan wadda aikin wata daya kacal tayi.
Da Ɗuminsa: Ba Za Mu Tafi Yajin aiki ba – NLC ta bayyana

Da Ɗuminsa: Ba Za Mu Tafi Yajin aiki ba – NLC ta bayyana

Siyasa
Shugaban kungiyar kwadago ta Najeriya (NLC), Joe Ajaero, ya bayyana cewa kungiyoyin kwadago ba za su tafi yajin aiki a ranar Talata ba, dangane da sabon takaddamar mafi karancin albashi da gwamnati ke fuskanta. Da yake bayar da dalilin daukar matakin, Ajaero ya ce har yanzu ma’aikata ba za su tafi yajin aikin ba saboda a halin yanzu alkaluman na kan teburin shugaban kasa Bola Tinubu kuma ana sa ran za a mayar da martani. Majiyar Jaridar Dimokuraɗiyya ta ruwaito shugaban NLC ya bayyana hakan ne yayin da yake magana a ranar Litinin a taron kungiyar kwadago ta duniya da ke gudana a birnin Geneva na kasar Switzerland. Yayin da yake buga misalan gwamnatocin da suka gabata, Ajaero ya ce har yanzu akwai yuwuwar Shugaban kasa ya kara adadin da ake so a gabansa. Sai dai ya yi kira ga Gw...
Ko Kudin Asusun Gwamnatin Kano Kwankwaso Ya Wawushe Baki Daya, Mu Kanawa Mun Yafe Masa, Inji Aisha Muhammad Adam

Ko Kudin Asusun Gwamnatin Kano Kwankwaso Ya Wawushe Baki Daya, Mu Kanawa Mun Yafe Masa, Inji Aisha Muhammad Adam

Siyasa
Ko Kudin Asusun Gwamnatin Kano Kwankwaso Ya Wawushe Baki Daya, Mu Kanawa Mun Yafe Masa, Inji Aisha Muhammad Adam A madadina da kuma sauran ragowar al'ummar jihar Kano ta dabo na zo na ari bakin kowa na ce albasa domin mika sako izuwa ga Maigirma Kwankwaso Madugu Uban Tafiya, Dan Musa Gagara Badau, cewa mu mutanen jihar Kano mun yafe maka koda a ce ka ci wannan kudin da ake fada ka ci, to mu mun yafe. Ka ci bagas, ka ci halak malak. Ai dama dukiyar ta mu ce mu kuma naka ne, to kaida kaya duk mallakar wuya ne. Yau a ce koda asusun gwamnatin Kano ka wawushe ka bar shi babu ko kwandala to mun yafe kasha kuruminka. Muna tare da kai, babu wanda za mu bari ya tozarta ka. Kanawa me za ku ce?

Zafin kan nono ga budurwa: Maganin zafin kan nono ga budurwa

Duk Labarai
Saka rigar mama da ta matse ki na iya kawo zafin kan nono, hakanan lokacin jinin Al'ada ma budurwa na iya yin fama da zafin nono. Tana iya yiyuwa ciwo ne ko kuma infection ya kamaki. Yawancin mata dake tsakanin shekaru 15 zuwa 40 na fana da ciwon kan nono. Wata kila tana iya yiyuwa magani ne kika sha ko kuma wani abinci ya miki reaction shiyasa kike jin hakan. Maganin zafin kan nono ga budurwa: Saka Rigar mama data yi daidai da nonoki zai taimaka wajan rage zafin. Zaki iya tanbayar likita ko me kemist ya baki magani. Rage shan chocolate, shayi, da lemunkan kwalba irinsu Fanta da Coke. Kina iya samun tsumma me sanyi ko dumi ki rika dorawa akan nonon. Motsa jiki akai-akai ma na taimakawa. Ki ragewa kanki damuwa da bacin rai. Lokacin da ya kamata ki ga likita ...
Babbar Sallah: ‘Yan Najeriya na kokawa kan tsadar dabbobi

Babbar Sallah: ‘Yan Najeriya na kokawa kan tsadar dabbobi

Duk Labarai
Babbar Sallah: 'Yan Najeriya na kokawa kan tsadar dabbobi. Yayin da babbar sallah ke ƙara ƙaratowa 'yan Najeriya na kokawa dangane da tsadar dabbobi musamman raguna waɗanda su ne aka fi amfani da su a lokacin layya. Wasu masu sayar da raguna da wakilin BBC a Legas ya tattauna da su sun ce farashin raguna ya ninka sau uku daga yadda aka sani a bara. "Ragon da aka saya a bara naira dubu 100 yanzu ya zama naira dubu 300. Haka shi ma na naira dubu ɗari biyu yanzu ya zama naira ɗari biyar". In ji wani mai sayarwa. Su ma masu sayen dabbobin da dama da aka tattauna da su sun ce bai zama lallai su yi layyar ba duk da dai wasu sun ce "amfani kuɗi shi ne a kashe su ta hanyar da ta dace."
Amurka ta fara janye sojojinta daga jamhuriyar Nijar

Amurka ta fara janye sojojinta daga jamhuriyar Nijar

Duk Labarai
Sojojin Amurka sun fara janyewa daga Nijar kamar yadda tashar talabijin ta ƙasar, Tele Sahel ta rawaito. A wani biki da aka yi a Air Base 101 da ke birnin Yamai, babban hafsan sojojin Nijar, Kanal Maj Mamane Kiaou, ya sanar da cewa, sojojin Amurka 260 daga cikin kiyasin 1,100 da aka kiyasta sun janye daga ƙasar tare da tankunan kayan aiki da dama. Maj Kiaou ya bayar da tabbacin cewa Nijar za ta tabbatar da tsaron jami'an Amurka a lokacin janyewar da ake sa ran kammalawa a tsakiyar watan Satumba. Duk da janyewar, ƙasashen biyu sun fitar da sanarwar hadin gwiwa a ranar 8 ga watan Yuni, inda suka tabbatar da cewa dangantakarsu ba za ta ɓaci ba. Janyewar sojojin ta biyo bayan sanarwar da gwamnatin mulkin sojan Nijar ta bayar a ranar 16 ga watan Maris, inda ta soke yarjejeniyar da t...
Gwamnatin jihar Plateau ta ɗage dokar hana yawo a Mangu

Gwamnatin jihar Plateau ta ɗage dokar hana yawo a Mangu

Tsaro
Gwamnatin jihar Filtao ta bayar da sanarwar dage dokar hana yawo da ta saka tun a watan Janairun wannan shekara a karamar hukumar mulki ta Mangu da kewaye. Gwamnan jihar Caleb Mutfwang ne ya saka dokar hana fitan har na tsawon awa ashirin da hudu a kowace rana, bayan wani hari da wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kai a kauyukan Punshit da Sabon-Gari inda suka kashe akalla mutum sha uku tare da jikkata karin wasu baya ga kona gidajen jama’a da dama. Gwamnatin Filaton ta bayyana cewa an saka dokar ne domin a samar da cikakken tsaro da zaman lafiya tsakanin kabilu daban-daban da ke fadin jihar.
Blinken a Masar don inganta yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza

Blinken a Masar don inganta yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza

Duk Labarai
Sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken ya isa Masar domin samun goyon bayan yankin ga yarjejeniyar zaman lafiyar Gaza da shugaba Joe Biden ya gabatar kwanan nan. Wannan ziyarar dai ita ce ziyara ta takwas da Blinken ya kai yankin Gabas ta Tsakiya tun bayan ɓarkewar rikicin Gaza. Blinken zai gana da shugaban Masar Abdel Fattah al-Sisi kafin ya tattauna da firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu a yau Litinin. Masu shiga tsakani a yankin ciki har da Qatar, sun shafe watanni da dama suna ƙoƙarin sasantawa tsakanin Isra'ila da Hamas. Netanyahu ya ci gaba da jajircewa wajen ƙin amincewa da duk wani tsagaita bude wuta har sai an wargaza sojojin Hamas da kuma sako duk waɗanda aka yi garkuwa da su. A karshen makon da ya gabata, sojojin Isra'ila sun kuɓutar da wasu mutane hu...