
Tsohon Mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar ya bayyana cewa, an masa kutse a asusun bankinsa an kwashe masa kudade.
Ya bayyana hakane a wata sanarwa da ya fitar ta bakin magana da yawunsa Frank Shu’aibu.
Atiku yace bayanan bankin nasa babu wanda ya san dasu amma sai gashi an kwashe masa kudade a ciki.
Yace idan mutum kamarsa za’a iya mai haka to lallai akwai matsala.