Monday, August 31
Shadow

Da Duminsa: An yi min kutse an kwashe min kudi a asusun bankina>>Inji Atiku Abubakar

Tsohon Mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar ya bayyana cewa, an masa kutse a asusun bankinsa an kwashe masa kudade.

Ya bayyana hakane a wata sanarwa da ya fitar ta bakin magana da yawunsa Frank Shu’aibu.

Atiku yace bayanan bankin nasa babu wanda ya san dasu amma sai gashi an kwashe masa kudade a ciki.

Yace idan mutum kamarsa za’a iya mai haka to lallai akwai matsala.

Karanta Wannan  Jihar Kaduna ta aika a Kwaso dalibanta dake jami'ar Jos saboda rashin tsaro

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *