
Rahotanni sun bayyana cewa, Hukumar ‘yansandan farin kaya ta DSS ta saka ranar da zata gurfanar da tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai a kotu.
Rahoton yace DSS sun saka ranar 25 ga watan Fabrairu dan gurfanar da El-Rufai a gaban kotu.
Za’a gurfanar dashine a gaban me shari’a, Joyce Abdulmalik bisa zargin kutse ma me baiwa shugaban kasa shawara kan harkar tsaro Malam Nuhu Ribadu a wayarsa.