
Gwamnatin tarayya ta bayyana jihohi 33 da kananan hukumomi 226 da ke fuskantar barazanar Ambaliyar ruwa a damunar bana.
Ministan ruwa da tsafta, Joseph Utsev ne ya bayyana hakan a yayin ganawa da manema labarai a Abuja.
Ya bayyana cewa, Jihohin da Ambaliyar ruwan zata faru sun hada da Abia, Adamawa, Anambra, Bauchi, Bayelsa, Benue, Borno, Cross River, Delta, Ebonyi, Edo, Enugu, Gombe, Imo, Jigawa, Kaduna, Kano, Kebbi, Kogi, Kwara, Lagos, Nasarawa, Niger, Ogun, Ondo, Osun, Oyo, Plateau, Rivers, Sokoto, Taraba, Yobe, Zamfara, da babban birnin tarayya, Abuja.
Ya bayyana cewa wasu garuruwan akwai hatsari me yawa wasu kuma kadan na faruwar ambaliyar ruwan.