
Rahotanni daga Kano na cewa, Dr. Rabiu Musa Kwankwaso ya watsar da Nasiru Yusuf Gawuna gefe a matsayin dan takarar gwamnan jihar Kano a jam’iyyar NDC.
Rahoton yace Kwankwaso ya zabi tsohon mataimakin Gwamnan jihar, Aminu AbdulSalam Gwarzo a matsayin dan takarar Gwamnan jihar ta Kano a jam’iyyar NDC.
Saidai Kwankwason bai bayyana hakan ba a hukumance, amma rahotanni nata yawo a kafafen sada zumunta game da hakan.
Inda wasu majiyoyi ke cewa, wasu na kusa da Kwankwaso sun tabbatar da hakan.