Friday, June 26
Shadow

Da Duminsa: Kwankwaso ya bayyana dan takarar Gwamnan jihar Kano karkashin jam’iyyar NDC kuma ba Gawuna bane

Rahotanni daga Kano na cewa, Dr. Rabiu Musa Kwankwaso ya watsar da Nasiru Yusuf Gawuna gefe a matsayin dan takarar gwamnan jihar Kano a jam’iyyar NDC.

Rahoton yace Kwankwaso ya zabi tsohon mataimakin Gwamnan jihar, Aminu AbdulSalam Gwarzo a matsayin dan takarar Gwamnan jihar ta Kano a jam’iyyar NDC.

Saidai Kwankwason bai bayyana hakan ba a hukumance, amma rahotanni nata yawo a kafafen sada zumunta game da hakan.

Inda wasu majiyoyi ke cewa, wasu na kusa da Kwankwaso sun tabbatar da hakan.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyon: A yayin da ake shirin yin zabe gobe a jihar Ekiti, An ga dan takarar APC na jefawa mutane Burodi daga mota yayin da su kuma suke bi suna wawa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *