
Tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana wata Mqarqashiya da yace ana shirya masa dan ci haba da tsareshi na tsawon lokaci.
Ya bayyana hakane ta bakin me magana da yawunsa, Muyiwa Adekeye inda yace Jaridar The Nation ta ruwaito cewa, wai daya daga cikin masu bayar da shaida akansa me suna Mohammed Umar Karage ‘yan Bindiga sun shiga gidansa.
Ya zargi cewa harin da aka kai masa bai rasa nasaba da shaidar da yake bayarwa akan malam Nasiru Ahmad El-Rufai.
Dan hakane Malam Nasiru Ahmad El-Rufai yace wannan bata sunane kuma ya baiwa lauyoyinsa umarnin su kai karar gidan jaridar.
Ya bayyana cewa bashi da hannun a harin da aka kaiwa shaidar nasa dan shi mutum ne me son bin doka da oda.