Monday, June 2
Shadow

Dansandan Najeriya ya Kkashe kansa

Dansandan Najeriya a Ofishin ‘yansandan dake Mada jihar Nasarawa ya harbi kanshi ya kashe kansa.

Rahotanni sunce a ranar da ya kashe kansa, anga dansandan me suna Dogara Akolo-Moses yana yawo abinsa.

Shaidu sun ce ya shiga wani daki ne ya kulle ya harbi kansa a cikin ofishinsu, kuma karar harbin da abokan aikinsa suka ji ne yasa suka ruga da gudu zuwa cikin dakin da yake.

Nan take suka iskeshi kwance a cikin jini.

Zuwa yanzu dai ba’a san dalilin da yasa ya kashe kansa ba.

Kakakin ‘yansandan jihar, Ramhan Nansel ya tabbatar da faruwar lamarin inda yace ana kan bincike.

Karanta Wannan  Ku Daina Gudun Talauci, Wani lokacin Talauci ma Wata Rahama ce daga Allah>>Kakakin Majalisar Dattijai, Sanata Godswill Akpabio ya baiwa 'yan Najeriya shawara

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *