
Kamfanin Meta iyayen Facebook da Instagram na barazanar ficewa daga Najeriya saboda yawan dokokin da gwamnatin tarayya ke gindaya musu.
Hakanan dayan dalilin da yasa kamfanin ke son ficewa daga Najeriya hadda harajin da ake kaka ba musu wanda suka ce yayi yawa.
Gwamnatin Najeriya ta maka kamfanin META a kotu akan zarge-zarge daban-daban inda take neman kamfanin ya biyata diyyar Dala Miliyan $290m, META sun shiga kotu amma basu yi nasara ba.
Kamfanin na Meta dai shine kuma ke da manhajar WhatsApp amma bai bayyanata cikin wanda zai kulle ba.
Kotun dai ta baiwa kamfanin nan da zuwa watan Yuni ya biya harajin da aka kakaba masa.