Wednesday, April 8
Shadow

Gwamnonin Arewa na taro kan matsalar tsaro a Kaduna

Gwamnonin arewa da kuma sarakunan gargajiya na gudanar da taro a Kaduna, domin tattaunawa kan matsalolin rashin tsaro da suka addabi yankin.

Taron wanda ke gudana a gidan gwamnatin jihar ta Kaduna, zai kuma tattauna kan matsalar talauci da yaran da ba su zuwa makaranta da kuma sauran al’amura da suke damun yankin.

Gwamnonin jihohin Zamfara da Kebbi da Gombe da Neja da kuma Zamfara na cikin waɗanda ke halartar taron.

A ɓangaren sarakunan gargajiya kuma akwai mai alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar III da Sarkin Zazzau, Ahmed Bamalli da Etsu na Nupe da Sarkin Zamfara da Sarkin Bauchi da Sarkin Ilorin da Sarkin Keffi da sauransu.

Karanta Wannan  Ji yanda wani yayi barazabar kulle asusun ajiyarsa da bankin Ja'iz saboda bankin basu tura masa sakon taya Maulidi ba, yace abin takaici shine sauran bankunan da bana Musulunci ba sun tura masa sakon taya murnar Maulidi amma banda Ja'iz

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *