Sunday, February 8
Shadow

Ji abinda Kwankwaso yace akan Abba game da zagayowar ranar Haihuwar gwamnan Kanon

Dr. Rabiu Musa Kwankwaso ya taya Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf murnar zagayowar ranar Haihuwarsa.

Ya wallafa sako a shafinsa na X inda yace yana Taya Abba Murnar zagayowar ranar Haihuwarsa.

Kwankwaso yace ya tuna irin yanda suna yi rayuwa tare da Abba inda ya masa mataimaki na musamman a lokacin yana Gwamna a zangon farko, hakanan sanda ya zama Ministan tsaro ya kuma tafi da abba a matsayin mataimaki na musamman.

Kwankwaso yace bayan nan ma kuma daya sake zama Gwamnan Kano, ya sake dauko abba a matsayin kwamishina kamin daga baya ya zama gwamnan Kano.

Kwankwaso yace sun yi aiki tare dan ciyar da jihar Kano gaba.

Karanta Wannan  Masha Allah: Kalli Bidiyon yanda su Ganduje da Sanata Barau suka musuluntar da wani babban jami'an Gwamnati a Abuja

inda yace yana masa fatan Alheri.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *