Friday, January 23
Shadow

Jirgin kasa dake jigila tsakanin Kaduna zuwa Abuja ya taka tare da kashe yara mata tagwaye a jihar Naija

Jirgin kasan daya taso daga Abuja zuwa Kaduna ya kashe kananan yaran wanda tagwayene mata a karamar hukumar Tafa.

Lamarin ya farune da misalin karfe 10 na safe ranar Asabar, kamar yanda jaridar The Cable ta ruwaito.

Yaran, Hassana and Hussaina Baro shekarar su daya da watanni 6.

Kakakin ‘yansandan jihar Naija, Wasiu Abiodun ya tabbatar da daruwar lamarin.

Yace yaran suna wasa ne akan titin jirgin kasan kamin lamarin ya faru.

Karanta Wannan  YANZU-YANZU: Kotu Ta Sallami Dukkannin Yaran Dake Tsare Saboda Zargin Zàñga-zàñgar Yunwa Da Tsadar Rayuwa, Bayan Babban Lauyan Ƙasa Ya Janye Tuhumar Da Gwamnati Ke Yi Musu

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *