Wednesday, January 7
Shadow

Kalli Bidiyo: ‘Yan Shi’a sun koka kan cirewa matansu hijabi da ‘yansanda suka yi a Abuja

Kungiyar ‘yan uwa musulmi da aka fi sani da shi’a aun koka kan cirewa matansu Hijabi da ‘yansanda suka yi a Abuja.

Kungiyar tace wannan cin zarafine da kuma batanci ga addinin musulunci.

Wakiliyar mata ta kungiyar ‘yan uwa musulmi, Maryam Sani ta bayyana a wata sanarwa data fitar cewa zasu yadawa duniya wannan lamari a gani.

Kuma zasu kai maganar kotu.

Bidiyo dai ya bayyana a kafafen sada zumunta inda aka ga ‘yansanda na cirewa matan ‘yan shi’ar Hijabi ta karfin tsiya.

Karanta Wannan  'Yan Fafutuka na kasashen Yarbawa sun bukaci a kama tsohon shugaban kasa, Janar Babangida a Hukuntashi

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *