
A yau ne dai hukumar tsaron farin kaya ta DSS ta janye karar data shigar akan malam Nasiru Ahmad El-Rufai inda ta zargeshi da yiwa wayar babban me baiwa shugaban kasa shawara akan harkar tsaro, Malam Nuhu Ribadu kutse.
Bayan janye karar, Lauyoyin Malam Nasiru Ahmad El-Rufai sun roki kotu da cewa, ta taimaka ta rage sharudan bayar da belin malam Nasiru Ahmad El-Rufai saboda sun yi tsauri.
Lauyoyin na Malam Nasiru Ahmad El-Rufai sun bayyana cewa, sun yi iya bincikensu basu samo ma’aikacin gwamnati dake mataki na 17 dake da gida a Maitama ba.
Lauyoyin sun kara da cewa, dan haka suna neman a sassauta sharudan bayar da belin na Malam Nasiru.
Saidai kotun ta yi watsi da wannan bukatar tasu inda DSS suka sake tasa keyar Malam Nasiru Ahmad El-Rufai suka tafi dashi.