
Tauraron fina-finan Hausa, kuma me bayar da Umarni, Dan Azumi baba, wanda aka fi sani da Kamaye ya bayar da labarin yanda ya sha da kyar a hannun Fusatattun matasa bayan da aka masa sharrin sacewa wani yaro golaye a Unguwar Kurna dake Kano.
Kamaye yace kawai yana tafiya sai ya dafa kafadar wani yaro sun taso daga makaranta, sai yaron ya ja da baya ya fasa ihu wai ya sacw masa balance dinsa.
Yace nan aka shiga dashi cikin makarantar akai ta dambarwa.
Da kyar aka samu aka fitar dashi.