Sunday, January 4
Shadow

Kalli Bidiyon: Kwankwaso ya bayyana cewa suna magana da wata jam’iyyar da yake son komawa amma ya saka musu sharadin sai sun bashi takarar shugaban kasa ko ta mataimakin shugaban kasa

Dr. Rabiu Musa Kwankwaso ya bayyana cewa, suna magana da wata jam’iyya inda yace zai koma cikinta.

Yace amma ya saka musu sharadin sai in sun yadda zasu bashi takarar shugaban kasa ko ta mataimakin shugaban kasa.

Ya bayyana hakane a wajan taron da aka yi a gidansa na ‘yan Kwankwasiyya a Kano.

Saidai bai bayyana sunan jam’iyyar ba.

A baya dai, Hutudole ya ruwaito muku da Thisday cewa, jam’iyyar ADC ce Kwankwaso ke shirin komawa.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyon Hauwa Kilishi ta labarina tana rawa data dauki hankula

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *