
Tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya sake Gurfana a gaban kotu a yau Litinin inda ake ci gaba da shari’ar kan zarginsa da almundahanar kudaden jihar lokacin yana kan mulki.
Kamar dai kullun, Jami’an tsaro sun tare hanyoyin dake kaiwa zuwa kotun da akewa malam Shari’a.
Saidai a zaman na yau, Sauran mutane 2 da ake musu shari’a tare da malam Nasiru Ahmad El-Rufai basu samu halartar zaman kotun ba wanda hakan yasa kotun ta daga zaman zuwa Ranar 24 ga watan Yuni.