
Tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya maka hukumar yaki da rashawa, ICPC a kotu inda yake neman su biyashi diyyar naira Biliyan 15.6 saboda bata masa suna.
Hakan na zuwane yayin da ICPC tace ta gano na’urar yiwa waya kutse a gidan malam Nasiru Ahmad El-Rufai.
Lauyoyin Malam Nasiru sun ce kalaman na ICPC abin damuwa ne kuma sun bata masa suna
Dan haka El-Rufai yace wannan abu ya take masa hakkinsa na Bil’adama inda yace yana neman.
Biliyan 15.6 na bata masa suna.
El-Rufai yace ya baiwa ICPC awanni 24 su gaggauta biyansa wannan kudi in ba haka ba zai makasu kotu.