Wednesday, April 29
Shadow

Matatar man fetur din Dangote zata fara fitar da man fetur din zuwa kasashen Africa guda 7

Rahotanni sun bayyana cewa, Matatar man fetur ta Dangote zata fara fitar da man fetur din zuwa kasashen Africa 7.

A yanzu dai matatar ta shirya tsaf dan fara fitar da man fetur din zuwa kasashen South Africa, Angola, da Namibia.

Sannan kuma tana tattaunawa da kasashen Niger Republic, Chad, Burkina Faso da Central Africa Republic dan fara kai musu man fetur din.

Hakana wata majiya tace akwai karin kasashe da ake sa ran zasu bayyana son daukar man fetur din na Dangote.

Misali kasar Ghana ma an bayyana cewa tana son fara magana da Dangote dan fara sayen man fetur dinsa.

Karanta Wannan  Bidiyo Gwanin Ban Tausai:Kalli Yanda 'Yan Damfara suka yiwa wani Alhaji Wayau suka kwace masa dala $1000 takardun dala $100 suka bashi dala $9 takardun dala daya-daya da sunan sun masa canji

Shugaban hukumar kula da man fetur ta kasar Ghana,Mustapha Abdul-Hamid ya bayyana cewa fara siyen man fetur din daga hannun Dangote zai sa su daina sayen man fetur din daga kasashen Turai

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *