Saturday, June 27
Shadow

Munin Tattalin arzikin Najeriya a yanzu yafi na lokacin da aka baiwa Najeriya ‘yanci a shekarar 1960>>Inji Shugaba Bankin Afrika

Shugaban bankin Afrika, AFDB, Dr Akinwumi Adesina ya bayyana cewa, lalacewar tattalin arzikin Najeriya a yanzu ya fi muni fiye da lokacin da aka baiwa Najeriya ‘yancin kai a shekarar 1960.

Ya bayyana hakanne a wajan wani taro da ya faru a Legas ranar Alhamis.

Yace Abinda ake cewa GDP per capital wanda shine ake auna ma’aunin tattalin arzikin kasa dashi a yanzu yana kan Dala $824 ne.

Yace a yayin da a lokacin da aka baiwa Najeriya ‘yancin kai a shekarar 1960 GDP per Capital yana kan Dala $1,847 ne.

Yace hakan ba karamar matsala bace inda yace ya kamata Gwamnatin Najeriya ta tashi tsaye dan shawo kan wannan matsalar.

Karanta Wannan  An kwacewa sanata Natasha Akpoti fasfo dinta an hanata fita kasar waje, Ta zargi Sanata Godswill Akpabio da sawa a mata hakan

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *