Friday, December 5
Shadow

Na ji dadin Fitowar Jam’iyyar ADC>>Inji Shugaban Ma’aikatan Fadar shugaba Tinubu, Femi Gbajabiamila, Ji dalilinsa

ADC: Gamaiyar am’iyyun adawa abu ne mai kyau da zai kare Najeriya daga mulkin jam’iyya ɗaya tilo– Gbajabiamila.

{“remix_data”:[],”remix_entry_point”:”challenges”,”source_tags”:[“local”],”origin”:”unknown”,”total_draw_time”:0,”total_draw_actions”:0,”layers_used”:0,”brushes_used”:0,”photos_added”:0,”total_editor_actions”:{},”tools_used”:{“square_fit”:1},”is_sticker”:false,”edited_since_last_sticker_save”:true,”containsFTESticker”:false}

Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Femi Gbajabiamila, ya bayyana cewa haɗin gwiwar jam’iyyun adawa tare da amincewa da jam’iyyar ADC a matsayin jam’iyyar su na kalubalantar jam’iyya mai mulki babban ci gaba ne da zai taimaka wajen ƙarfafa dimokuraɗiyya a ƙasar.

Gbajabiamila ya bayyana haka ne a ranar Asabar yayin da yake zantawa da manema labarai bayan kada ƙurarsa a rumfar zaɓe ta PU 014 dake makarantar Elizabeth Fowler Memorial High School a unguwar Adeniran Ogunsanya, Surulere, yayin zaɓen ƙananan hukumomi a jihar Legas.

Ya ce: “Wannan wani ci gaba ne mai kyau tare da haɗin ƙawancen. Ba sabon abu bane muna ganin haka. Duk wata dimokuraɗiyya tana buƙatar samun adawa a wani mataki, in ba haka ba ƙasar za ta iya shiga mulkin jam’iyya ɗaya. Amma ban tabbata inda wannan zai kai mu ba.”

Karanta Wannan  Ina Nan A Raye Amma Ba A Kulle Nake Ba, Batun Kamu Kuma A Koda Yaushe Za A Iya Kama Ni, Kuma A Shirye Nake Koda Zan Ŕàsà Raiña, Tunda Dama Sùn Jimà Suña Ñemañ Rabà Nì Da Rayùwațà, Kuma Ina Godiya Da Addù'o'inku Masoyana, Inji Odinari Ahmed Isa

A farkon wannan watan, jagororin ƙawancen jam’iyyun adawa sun taru a Cibiyar Yar’Adua dake Abuja, inda suka bayyana hukuncin ɗaukar ADC a matsayin jam’iyyar su na kalubalantar APC a babban zaɓen shekarar 2027.

A wajen taron, shugaban jam’iyyar ADC, Ralph Nwosu, ya mika katin membobinsu ga tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, David Mark, da tsohon Gwamnan Osun, Rauf Aregbesola, waɗanda aka gabatar a matsayin shugaban rikon kwarya na jam’iyyar da kuma sakataren jam’iyya na ƙasa.

Fitattun ’yan siyasa da suka halarci taron sun haɗa da tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar; ɗan takarar jam’iyyar Labour Party a 2023, Peter Obi; tsoffin gwamnoni Nasir El-Rufai da Rotimi Amaechi; da sauran manyan ’yan siyasa kamar Dino Melaye, Dele Momodu, Solomon Dalung, Sanata Gabriel Suswam, Sanata Ireti Kingibe, Emeka Ihedioha, da Air Marshal mai ritaya Sadique Abubakar.

Karanta Wannan  Ku zabeni, na yi Alkawarin wa'adi daya kawai zan yi in sauka>>Peter Obi

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *