Tuesday, August 18
Shadow

NAHCON ta kammala jigilar alhazan Najeriya daga Saudiyya

Hukumar Alhazan Najeriya ta kamala jigilar alhazan ƙasar da suka sauke farali a aikin hajjin bana.

Cikin wata sanarwa da hukumar ta wallafa a shafinta na X, ta ce ta kammala aikin kwaso alhazan daga ƙasa mai tsarki a yau Laraba 2 ga watan Yulin 2025.

Kimanin alhazan Najeriya 41,291 ne suka sauke farali a wanan shekara, kamar yadda hukumar ta bayyana.

Jirgin ƙarshe da ya ɗauko alhazan jihar Kaduna ya taso da safiyar yau.

Karanta Wannan  Kalli Yanda matan da ake zargin an baiwa kudi dan su fito tarbar shugaba Tinubu a Kaduna ke kulle fuskokinsu basu son kyamara ta daukesu hoto

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *