Friday, July 17
Shadow

Najeriya ta samu tsaro sosai a zamanin mulkin Tinubu >>Inji me magana da yawun shugaban kasa, Daniel Bwala

Me baiwa shugaban kasa shawara kan harkar sadarwa, Daniel Bwala ya bayyana cewa, An samu tsaro sosai a Najeriya a mulkin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu.

Ya bayyana hakane a hirar da aka yi dashi a gidan talabijin na Channels TV.

Daniel Bwala yace kamin hawan shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu mulki ana garkuwa da mutane yanda aka ga dama har cikin Abuja da rana tsaka ana garkuwa da mutane amma wannan duk ya kau.

Yace an fasa gidajen yari da dama a mulkin baya amma a zamanin Tinubu lamura sun gyaru

Karanta Wannan  Kalli Bidiyo: Maganar Gaskiya Yawancin Masu Kallon Mu Ba Su Da Cikaķķen Ilmi, Inji Jarumar Finafinan Hausa, Zahra Diamond

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *