Yayin da aka kamma wasannin Quarter finals.
Arsenal da PSG ne zasu hadu a wasan kisa dana karshe da za'a buga.
Sai kuma Barcelona zata hadu da Inter Milan.
Wasannin Farko za'a buga su ne ranar 29 zuwa 30 ga watan Afrilu inda wasannin zagaye na biyu za'a bugasu ne ranar 6 da 7 ga watan Mayu.
Wasu mahara da ake zargin ƴanbindiga ne masu ikirarin jihadi sun kashe sojoji takwas a arewacin ƙasar Benin, kamar yadda majiyar tsaro ta shaida wa AFP a ranar Juma'a.
Harin ya auku ne a sansanonin sojojin ƙasar guda biyu a ranar Alhamis, sai dai majiyar ta ƙara da cewa an kashe maharan guda 11 a gwabzawar.
Waɗanda suka jikkata yanzu suna kwance suna jinya a wani asibiti a ƙasar.
Sojojin Benin dai suna cigaba da gwabza yaƙi a yankin ne domin fatattakar ƴanbindiga, inda ko a Janairun 2022 ta aika ƙarin sojoji 3,000.
Ko a watan Janairun da ya gabata an kashe sojojin Benin 29 a wani hari da ƙungiyar GSIM mai alaƙa da Al Qaeda ta ɗauki alhaki.
Tsohon Ministan Shari'a na Najeriya, Dakta Abubakar Malami, SAN, ya yi watsi da iƙirarin da wasu ƴan tsohuwar jam'iyyar CPC - da ta narke cikin haɗakar APC - suka yi na nesanta tsohuwar jam'iyyar daga ficewa daga haɗakar.
A farkon makon nan ne wani tsagin tsohuwar jam'iyyar CPC ƙarƙashin jagorancin tsohon gwamnan Nasarawa, Umaru Tanko Almakura suka yi taro a Abuja, inda suka jaddada goyon bayansu ga gwamnatin shugaba Tinubu tare da nesanta kansu daga ficewa daga APC.
Daga cikin waɗanda suka harci taron har da tsohon gwamnan Katsina, Aminu Bello Masari da tsohon ministan Ilimi, Mallam Adamu Adamu da Hon Farouk Adamu Aliyu, tsohon ɗan majalisar daga jihar Jigawa da wasu ƙusushin tsohuwar CPCn.
To sai toshon Ministan ya yi watsi da wannan iƙirari da tsagin Almakuran suka yi, yana mai...
Ministan Abuja, Nyesom Wike ya ce babbar jam'iyyar hamayyar ƙasar, PDP ba ta da kyakkyawan shiri da tsarin kayar da APC a zaɓen 2027 ba.
Yayin da yake jawabi a wata ganawa da manema labarai a Abuja, ranar Juma'a, tsohon gwamnan na jihar Rivers ya ce a yanayin da jam'iyyar PDP ke ciki a halin yanzu ba za a ce ta shirya wa zaɓen 2027, saboda rikicin shugabanci da jam'iyyar ke ciki.
''PDP ba ta shirya wa zaɓen 2027 ba, wannan a bayyane yake. Ga yadda suke tafiya a yanzu rikicin jagoranci na ci gaba da yi wa jam'iyyar tarnaƙi'', in ji shi.
A baya-bayan nan dai wasu daga jam'iyyun hamayyar ƙasar ciki har da PDp na ƙoƙarin samar da wata haɗaka domin tunkarar APC a 2027.
To sai dai da alama tafiyar na ci gaba da fuskantar tasgaro, saboda muradun wasu ƴansiyasar.
Jami'an hukumar hana sha da fataucin miyagun Kwayoyi, NDLEA sun fuskanci matsalar harin kwantan Bauna da aka kai musu yayin da suka kai samame kan wasu masu harkar miyagun kwayoyi a Jahi dake Abuja.
Jami'an NDLEA sun kai samamenne bayan da suka samu bayanan sirri game da harin inda suka shiga wani kango suka kwace kwayoyin.
Saidai a yayin da suke shirin ficewa daga cikin kangon, maharan sun bude musu wuta inda aka jikkata ma'aikatan hukumar su 3.
Daya daga cikin ma'aikatan an sameshi ne a kirjinshi inda daya kuma sauran aka samesu a kafa.
Tuni dai aka garzaya dasu Asibiti dan basu kulawa ta musamman.
Shugaban hukumar, Brig Gen Mohamed Buba Marwa (Rtd) ya jinjinawa ma'aikatan asibitin Abuja bisa kulawar da suka baiwa ma'aikatansa inda kuma yayi magana da wadanda aka jikka...
FASAHA: Matashi Ya Kirkiri Na'urar Dake Gano Makamai Ko Ma'adanai A Cikin Dakika Daya.
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false}
Matashi dan asalin kljihar Kano mai suna Khalifa Aminu ya kirkiri na'urar dake gano makamai da ma'adinai dake ƙarƙashin ƙasa.
Na'urar za ta iya gano makamai waɗan da aka binne akarkashin kasa, da kuma ma'adanai dake ƙarƙashin ƙasa.
Wasu daga cikin abubuwan da na'urar zata iya gano wa, sun haɗa da, Gün, Bôóm, Bûllet dai sauran ma'adinai dake ƙarƙashin ƙasa.
Daga Ibrahim Dau Dayi...
Wasu da ake zargin ƴan fashin jeji ne sun kai hari garin Faruruwa da ke Karamar Hukumar Shanono a Jihar Kano, inda suka kashe mutane biyu tare da yin garkuwa da wasu da ba a bayyana adadinsu ba.
Majiyoyi sun bayyana cewa maharan sun kai harin ne a kasuwar garin da misalin karfe 7 na dare a jiya Alhamis, inda suka fara harbe-harbe kan me uwa da wabi.
Wani shaida, Ibrahim Faruruwa, ya ce maharan sun yi yunkurin sace wani hamshakin dan kasuwa, Alhaji Haruna Halilu, sai dai ba ya shagon nasa a lokacin harin.
Ya ce: “Da basu samu Alhaji Haruna ba, kawai sai suka sace dansa, Mas’ud.”
Ya kara da cewa maharan sun kashe mutane biyu — wato Alhaji Rabiu Faruruwa da Sahabi Dankwaro a yayin harbe-harben da su ka riƙa yi.
Wani mazaunin garin, Abubakar Hamza Adam, ya ce dan uwansa karami, ...
Dillalan man fetur da masana sun bayyana dalilan da suka sa ba a ganin sauƙin kirki na man fetur a gidajen mai duk da faɗuwar fashin gangar mai a kasuwar duniya.
Ƴan Najeriya a yanzu na sayen man fetur tsakanin N940 zuwa N970 a Abuja babban birni ƙasar.
Farashin gangar ɗanyen mai ya sauka a kasuwar duniya sakamakon yakin kasuwanci da shugaba Trump na Amurka ya ƙaddamar kan China da sauran ƙasashen duniya, inda ake sayar da ganga kan dala 61 zuwa 65.
Kodayake a ranar Laraba farashin ɗanyen man ya ƙaru bayan sabbin takunkuman Amurka kan man Iran da ake shigar wa China.
Rikicin haraji ya rage buƙatuwar man fetur a duniya saboda raguwar samar da abubuwa, dalilin da ya sa man fetur ya yi arha a Najeriya da sauran ƙasashe.
Sai dai kuma wasu na ganin ya kamata sauƙin ya fi wanda ak...
Manyan ƴan siyasar Najeriya da ke jagorantar shirin yin haɗaka tsakanin jam'iyyun hamayya domin tunkarar APC a zaɓen 2027, sun mayarwa ƙungiyar gwamnonin jam'iyyar PDP martani, a kan matsayar da gwamnonin suka ɗauka cewa ba su goyon bayan ƙulla duk wata haɗaka da za ta fitar da su daga PDP.
Gamayyar ƴan adawar da ta haɗa da tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar da ɗan takarar shugaban ƙasa na jam'iyyar Labour a zaɓen 2023 da tsohon gwamnan jihar Kaduna Malam Nasir El-Rufai da dai sauran ƴan siyasa, ta ce nan ba da jimawa ba za a sanar da ƙulla sabuwar haɗakar siyasa da za ta ceto Najeriya daga mulkin APC.
Ɗaya daga cikin jagororin tafiyar ƙulla sabuwar haɗakar siyasar ta Najeriya kuma tsohon mataimakin shugaban jam'iyyar APC na ƙasa mai kula da shiyyar Arewa Maso Yamma, Sali...
Hukumar Tace Fina-finai da Dab’i ta Jihar Kano ta kaddamar da wani sabon atisayen kama baburan adai-daita sahu da ke dauke da hotunan batsa da rubuce-rubuce marasa tarbiyya a manyan titunan jihar.Shugaban hukumar, Alhaji Abba El-Mustapha, ne ya tura jami’an sa don gudanar da wannan aiki, inda ya bayyana cewa hakan na daga cikin nauyin da ke kan hukumar na tabbatar da tsaftar hotuna da rubuce-rubuce da ke bayyana a fili ga al’umma.Sanarwar ta fito ne daga Abdullahi Sani Sulaiman, Jami’in Hulda da Jama’a na Hukumar Tace Fina-finai da Dab’i ta Jihar Kano.“Aikinmu shi ne tabbatar da cewa babu wani hoto ko rubutu da zai cutar da tarbiyya ko dabi’un al’umma, musamman matasa, ya fito fili ba tare da tantancewa ba,” in ji Abba El-Mustapha.Daraktan Sashen Dab’i na hukumar, Alhaji Abub...