Friday, February 20
Shadow
Kalli Bidiyon: Majalisa ta kammala tantance Dambazau da FFK a matsayin jakadu

Kalli Bidiyon: Majalisa ta kammala tantance Dambazau da FFK a matsayin jakadu

Duk Labarai
Majalisar Dattijai ta kammala tantance Femi Fani Kayode da Abdulrahman Dambazau a matsayin jakadu wanda shugaba Tinubu zai aika kasar waje. A baya dai dukansu sun taba zuwa majalisar inda aka tantancesu, shiyasa yanzu da suka je sai majalisar tace musu kawai su wuce. https://twitter.com/Imranmuhdz/status/1999092298504933606?t=YAkZeDxEXKAkUlSQcV3xZA&s=19 https://twitter.com/Imranmuhdz/status/1999119860899418599?t=Yb9U7kI6UM1vdlBGvKBy3w&s=19
Kalli Bidiyon: Trump ka gaggauta ka zo kamin su gama damu, yanzu haka ma sun sa an rufe min shafina na Facebook>>Rev. Ezekiel Dachomo ya bayyana

Kalli Bidiyon: Trump ka gaggauta ka zo kamin su gama damu, yanzu haka ma sun sa an rufe min shafina na Facebook>>Rev. Ezekiel Dachomo ya bayyana

Duk Labarai
Malamin Kirista, Rev. Ezekiel Dachomo ya roki shugaban kasar Amurka, Donald Trump ya gaggauta ya zo Najeriya inda yace yazo kamin a gama dasu. Ya kawo misalin cewa yanzu haka shi an sa an rufe masa shafinsa na Facebook. Rev. Ezekiel Dachomo dai na daya daga cikin na gaba-gaba dake son Kasar Amurka ta kawo dauki Najeriya. https://twitter.com/ezekieldachomo0/status/1999081251916112013?t=icVkjZj14fTLkkkayG2uPg&s=19
Kalli Bidiyon yanda hàtsànìyà ta kaure a majalisa aka so a baiwa Hammata Iska saboda gayyatar gwamnan CBN saboda batan Naira Triliyan 11>>Wasu ‘yan majalisar sun yadda a gayyaceshi inda wasu suka ce basu yadda ba

Kalli Bidiyon yanda hàtsànìyà ta kaure a majalisa aka so a baiwa Hammata Iska saboda gayyatar gwamnan CBN saboda batan Naira Triliyan 11>>Wasu ‘yan majalisar sun yadda a gayyaceshi inda wasu suka ce basu yadda ba

Duk Labarai
' Yan majalisar Wakilai sun tattauna bukatar gayyatar gwamnan babban bankin Najeriya, CBN, Cordoso saboda zargin batan wasu kudade har Naira Tiriliyan 11. Saidai kan 'yan majalisar ya rabu inda wasu suka amince a gayyaci gwamnan CBN din wasu kuma sun ce basu amince ba. Muhawara ta yi zafi akan hakan inda aka rika gayawa juna magana da nuna yatsa. https://twitter.com/thecableng/status/1998841059497934985?t=CgGvcKBNth4voAhpc76kmg&s=19
Hukumar ‘yansandan Najeriya ta yi magana kan dansandan da aka ga matasa na Dùqànsà saboda zargin yayi sàtà

Hukumar ‘yansandan Najeriya ta yi magana kan dansandan da aka ga matasa na Dùqànsà saboda zargin yayi sàtà

Duk Labarai
Hukumar 'yansandan Najeriya ta yi magana kan dansandan da aka ga ana dukan sa akan titin Legas bisa zargin sata. Me magana da yawun 'yansandan jihar Legas, Abimbola Adebisi ne ya bayyana cewa suna bincike kan lamarin. Bidiyon ya watsu sosai a kafafen sada zumunta inda aka ga dansandan jina-jina matasa na dukansa suna kiransa ds Barawo.
Mun gana da Kiristoci da ke zaune a sansanin ‘yan gudun Hijira ba zamu kyale Fulani da suka sakasu a wannan halin ba dole mu dauki mataki akansu>>Inji ‘yan majalisar kasar Amurka da suka kawo ziyara Najeriya

Mun gana da Kiristoci da ke zaune a sansanin ‘yan gudun Hijira ba zamu kyale Fulani da suka sakasu a wannan halin ba dole mu dauki mataki akansu>>Inji ‘yan majalisar kasar Amurka da suka kawo ziyara Najeriya

Duk Labarai
' Yan majalisar kasar Amurka da suka kawo ziyara Najeriya wanda Riley Moore ya musu jagora sun ce sun gana da Kiristoci da aka yiwa cin zarafi a jihar Benue. Sun ce sun gan su a matsayi na rashin tabbas wanda suka zargi Fulani da jefasu a ciki. Riley yace ba zasu zuba ido suna ganin irin wannan abuba, dole zasu dauki mataki. Yace ya ji labarai masu tayar da hankali da 'yan Gudun Hijirar suka gaya masa wadanda ba zai taba mantawa dasu ba.
Kaso 35 cikin 100 na ruwan Najeriya ne kadai sojojin ruwa suke iya tsarewa, sauran Kamfanoni masu zaman kansu aka dauka aka baiwa kwangilar aikin>>Inji Sowore

Kaso 35 cikin 100 na ruwan Najeriya ne kadai sojojin ruwa suke iya tsarewa, sauran Kamfanoni masu zaman kansu aka dauka aka baiwa kwangilar aikin>>Inji Sowore

Duk Labarai
Dan Gwagwarmaya kuma dan siyasa, Mawallafin Jaridar Sahara Reporters, Omoyele Sowore ya bayyana cewa, Sojojin Ruwan Najeriya kaso 35 cikin 100 ne kawai na ruwan Najeriya suke iya tsarewa. Ya bayyana cewa, sauran wasu kamfanoni ne masu zaman kansu aka baiwa suke kula da tsaron ruwan kasar. Ya bayyana hakane a wata hira da aka yi dashi inda yake magana akan gazawar jami'an tsaron Najeriya. https://twitter.com/OzorNdiOzor/status/1998731226077692252?t=uOX7B2O65QJm4gFoSh5x4g&s=19