Saturday, March 14
Shadow
Buhari ya yadda da Rade-Radin da aka rika yadawa cewa wai zan Shyèkyè shi>>Inji A’isha Buhari

Buhari ya yadda da Rade-Radin da aka rika yadawa cewa wai zan Shyèkyè shi>>Inji A’isha Buhari

Duk Labarai
Matar tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari, Hajiya Aisha Buhari ta bayyana cewa, marigayi mijin nata ya amince da cewa tana son kasheshi. Tace an rika yada rade-radin cewa, tana son ta kashe Mijin nata a fadar shugaban kasar inda tace har ta kai ga Buharin ya fara yadda da abinda mutanen ke cewa. Tace Buhari ya canja mata kwata-kwata ya rika kulle kofa da sauransu. Tace rashin lafiyar da yayi na da alaka da canjin abinci da rashin samun abinci me gina jiki. Tace amma da aka kaishi kasar waje ya samu sauki. Tace babu gaskiya a maganar cewa, guba ce aka sawa Buharin.
Karin bayani game da halin da kakakin majalisar Dattijai Godswill Akpabio ke ciki bayan da a Yànkyè jìykyì ya fàdì aka garzaya dashi Asibitin Landan

Karin bayani game da halin da kakakin majalisar Dattijai Godswill Akpabio ke ciki bayan da a Yànkyè jìykyì ya fàdì aka garzaya dashi Asibitin Landan

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Kakakin majalisar Dattijai, Godswill Akpabio na can asibiti a birnin landan inda yake jinya. Hutudole ya ruwaito muku jiya cewa, Akpabio ya yanke jiki ya fadi ne inda Sabbin Rahotannin da muka sau suka ce Dangote ya bayar da jirgi aka tafi dashi Landan inda yake jinya. Kuma mun samu cewa Lamarin ya farune ranar 10 ga watan Disamba, kamar yanda Sahara Reporters ta ruwaito. Hutudole ya fahimci cewa, Likitoci sun ce Aiki ne yawa Akpabio yawa shiyasa wannan lamari ya sameshi, da haka suke bashi shawarar ya ajiye aiki ya koma ya kula da lafiyarsa. Akpabio dai an ganshi a karshe a zauren majalisar tun ranar da majalisar ta amincewa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya aika da sojoji kasar Benin Republic.
Kalli Bidiyon: Indai da Hausa kake Waka, Nine Sarkin Ka>>Inji Dauda Kahutu Rarara

Kalli Bidiyon: Indai da Hausa kake Waka, Nine Sarkin Ka>>Inji Dauda Kahutu Rarara

Duk Labarai
Tauraron mawakin Siyasa, Dauda Kahutu Rarara ya bayyana cewa, indai da Hausa mutum yake waka a yanzu ya zama sarkinsa. Ya bayyana hakane a wata hira da aka yi dashi bayan nadin Sarautar Sarkin Mawakan Hausa da aka masa a garin Daura na jihar Katsina. Rarara Yace a zahirin Gaskiya shi yama fi iya wakokin Sarauta. https://www.tiktok.com/@darrusy/video/7584178222812663047?_t=ZS-92Fned67WBU&_r=1
Kalli Bidiyon yanda aka Kai Rahama Sadau dakin Mijinta

Kalli Bidiyon yanda aka Kai Rahama Sadau dakin Mijinta

Duk Labarai
Tauraruwar fina-finan Hausa, Rahama Sadau kenan a yayin da aka kai ta dakin Mijinta bayan da tun tuni aka daura auren. An ga dai yanda ta yi shagalin bikin ita da 'yan uwanta kadai babu 'yan fim a wajan bikin. https://www.tiktok.com/@queenhajjarh/video/7584129039028276488?_t=ZS-92FkS2Q85K4&_r=1 https://www.tiktok.com/@arewa_family_weddings/video/7583472614220320021?_t=ZS-92FjlBlklnN&_r=1
Dangote ya zargi shugaban Hukumar kula da mab Fetur  NMDPRA Engr. Farouk Ahmed da biyawa ‘ya’yansa kudin makaranta Dala Miliyan $5

Dangote ya zargi shugaban Hukumar kula da mab Fetur NMDPRA Engr. Farouk Ahmed da biyawa ‘ya’yansa kudin makaranta Dala Miliyan $5

Duk Labarai
Attajirin Najeriya, Aliko Dangote ya zargi shugaban Hukumar kula da man fetur ta kasa, NMDPRA Engr. Farouk Ahmed da kai 'ya'yansa makaranta kasar Switzerland inda yace ya biya musu dala Miliyan $5. Dangote yace wanda ke daukar Albashi ina ya samu irin wadannan kudade. Yace koshi 'ya'yansa ba zai biya musu irin wadannan makudan kudade ba lura da cewa a Kano akwai yaran da basa iya zuwa makaranta. Dangote yace akwai masu neman karyashi da hana matatar man fetur dinsa yin aiki yanda ya kamata. https://twitter.com/shatou__/status/2000589268004020727?t=hcP_dK5skoyVPk-xadOZvw&s=19
Tsohon Ministan Kwadago, Chris Ngige ya nemi Beli inda yace yana fama da rashin lafiya bayan da kotu tace a tsareshi a gidan yarin Kuje, amma EFCC tace kada a bada belinsa dan zai iya tserewa

Tsohon Ministan Kwadago, Chris Ngige ya nemi Beli inda yace yana fama da rashin lafiya bayan da kotu tace a tsareshi a gidan yarin Kuje, amma EFCC tace kada a bada belinsa dan zai iya tserewa

Duk Labarai
Tsohon Ministan Kwadago Chris Ngige ya nemi Beli bayan da Kotu tasa a daureshi a gidan yarin Kuje. Yace yana fama da rashin lafiya, kamar yanda Lauyansa, Patrick Ikwueto ya bayyanawa me shari'a ta babbar kotun tarayya dake Gwarimpa a Abuja Justice Maryam Aliyu Hassan Saidai Lauyan EFCC, Sylvanus Tahir, SAN yace kotun kada ta bayar da belinsa dan a baya ita EFCC ta sakeshi inda aka saka mai ranar da zai sake komawa dan ci gaba da bincike amma yaki komawa. Yace tsohon Ministan ka iya tserewa idan aka bayar da belinsa. Saidai Mai shari'a Maryam Aliyu Hassan tace a ci gaba da tsare Ngige a gidan yarin kuje har ranar 18 ga watan Disamba kamin ta yanke hukunci kan maganar Belin.
Kalli Bidiyon: Tinubu ba zai ci zabe a 2027 ba>>Inji Sanata Enyinnaya Abaribe

Kalli Bidiyon: Tinubu ba zai ci zabe a 2027 ba>>Inji Sanata Enyinnaya Abaribe

Duk Labarai
Sanata Enyinnaya Abaribe ya bayyana cewa, shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ba zai ci zabe ba a shekarar 2027. Ya bayyana hakane a hirar da Jaridar Channels TV ta yi dashi. Yace ko da a zaben 2023 Tinubu ba zabe yaci ba. Yace yana da yakinin Tinubu ba zai ci zabe bane saboda yanda mutane ke cikin wahala a gwamnatinsa. https://twitter.com/channelstv/status/2000637809325908386?t=zYn2EMO6acuG-s3FgP_n2A&s=19