Saturday, December 13
Shadow
Kalli Bidiyo: Sheikh Musa Asadussunnah yace kamar yanda ake shirin Titsiye, Malam Lawal Triumph a hada da Malam Nazifi Alkarmawi saboda yace idan mutum yayi mafarki ya ga Raqumi, Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) ya gani

Kalli Bidiyo: Sheikh Musa Asadussunnah yace kamar yanda ake shirin Titsiye, Malam Lawal Triumph a hada da Malam Nazifi Alkarmawi saboda yace idan mutum yayi mafarki ya ga Raqumi, Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) ya gani

Duk Labarai
Malam Musa Asadussunnah ya bayyana cewa, idan dai za'a Titsiye malam Lawal Triumph kan kalaman da yayi, to ya kamata a Hada da malam Nazifi Alkarmawi. Malam Musa yace, Shima Alkarmawi yace idan aka yi mafarkin Raqumi to kamar an ga Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) ne. Yace amma babu wanda yaji yana sukar Alkarmawi aka wannan kalamai. Yace dan haka indai za'a titsiye malam Lawal Triumph to a hada da Alkarmawi. https://www.tiktok.com/@buharimandemgy/video/7555596889450630418?_t=ZS-909Y9F2iVEH&_r=1 https://www.tiktok.com/@muhammadsunnahaljosawy/video/7555545750835350802?_t=ZS-909bl2Injmb&_r=1
Babu ruwan mu da ta Halal ko ta Haram ka samu kudin shiga, Kowa, hadda Kharuwaiy sai sun fara biyan Haraji nan da shekarar 2026>>Inji Gwamnatin Tarayya

Babu ruwan mu da ta Halal ko ta Haram ka samu kudin shiga, Kowa, hadda Kharuwaiy sai sun fara biyan Haraji nan da shekarar 2026>>Inji Gwamnatin Tarayya

Duk Labarai
Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa sabuwar dokar Haraji da zata fara aiki a shekarar 2026 ba ruwanta da anda mutum ya samu kudi, ko ta hanyar data kamata mutum ya samu ko bata hanyar dta kamata ba, dole ya biya Haraji. Shugaban Kwamitin shugaban kasa kan tsare-tsaren kudi da Gyara, Taiwo Oyedele ne a bayyana haka a cocin RCCG a wata ziyara da ya kai. Yace idan dai mutum zai sayar da wani abu ko zai aikata wani abu ya samu kudi, ba ruwan gwamnati da wane irin aiki ne mutum ya aikata, sai ya biya Haraji, kamar yanda kafar Peoplesgazette ta ruwaito. Gwamnatin tarayya dai na kokarin ganin ta karbi haraji daga kowane fanni na samun kudi dan ta tayar da komadar tattalin arzikin Najeriya.
Kalli Bidiyo: Saurayinta ya siyo mata wayar iPhone XR amma tace bata so sai dai ya siyo mata iPhone 13

Kalli Bidiyo: Saurayinta ya siyo mata wayar iPhone XR amma tace bata so sai dai ya siyo mata iPhone 13

Duk Labarai
Wannan wata matashiyace da ta jawo cece-kuce bayan da saurayinta a sai mata wayar iPhone XR amma tace bata so sai 13. A Bidiyon da ya watsu sosai, an ji yana cewa ta ce masa bata son iPhone X, shine ya kawo mata XR amma itama tace bata so ya kaiwa mabukata. Da yawa dai sun yi mamakin rashin godiyar Allah na Budurwar. Kalli Bidiyon anan
Dan Najeriya da aka turawa Dala dubu 135 cikin wallet dinsa ta Kyriptho, watau Kwatankwacin Naira Miliyan 200 bisa kuskure ya mayar wa da me kudin kayansa

Dan Najeriya da aka turawa Dala dubu 135 cikin wallet dinsa ta Kyriptho, watau Kwatankwacin Naira Miliyan 200 bisa kuskure ya mayar wa da me kudin kayansa

Duk Labarai
Dan Najeriya, Sunusi Danjuma Ali da aka turawa Dala dubu 135 a wallet dinsa na Crypto watau kwatankwacin Naira Miliyan 200 bisa kuskure ya mayarwa da me kudin kudinsa. An tura masa kudinne a Wallet dinsa ta Bitunix inda yana ganin hakan ya tuntubi wakilan kamfanin kuma suka tabbatar kuskurene aka yi wajan tura masa kudin. Nan da nan aka warware.
Kawuna a Legas yake zaune amma baya cin kifin da ake sayarwa a Legas, Kullun Idan zai ci kifi, Landan yake aikawa a siyo mai a doro a jirgin sama a kawo mai>>Inji Dan Forex, Dapo Wills

Kawuna a Legas yake zaune amma baya cin kifin da ake sayarwa a Legas, Kullun Idan zai ci kifi, Landan yake aikawa a siyo mai a doro a jirgin sama a kawo mai>>Inji Dan Forex, Dapo Wills

Duk Labarai
Shahararren dan Forex, Dapo Wills ya bayyana cewa, Kawunsa na zaunene a Legas amma idan zai ci Kifi, baya cin wanda ake sayarwa a Legas. Yace Landan yake aikawa a siyo kifin a sako mai shi a jirgi sannan a kawo ya ci. Ya bayyana hakane a wata hira da aka yi dashi wadda ta watsu sosai a kafafen sadarwa. Kalli Bidiyon hirar a kasa: https://twitter.com/Teeniiola/status/1972242656970649655?t=ZnQXjyJyQe7-vNRxx9miVg&s=19
Lamari Ya Munana: Kungiyar PENGASSAN dakatar da ayyukan tace mai a matatar Man fetur ta Dangote

Lamari Ya Munana: Kungiyar PENGASSAN dakatar da ayyukan tace mai a matatar Man fetur ta Dangote

Duk Labarai
Rahotanni sun tabbatar da cewa Kungiyar PENGASSAN ta manyan ma'aikatan man fetur ta dakatar da aikin tace man fetur a matatar man Dangote. Rahoton yace A yanzu ayyuka sun tsaya cik a matatar man fetur din. Hakanan lamarin ya shafi bangaren yin takin zamani. Saidai PENGASSAN tace ta bar wani bangare na Gas a ma'aikatar dake aikin kaso 60 cikin 100. Matatar ta dauki wannan mataki ne dan matsawa masu gudanarwa na matatar su mayar da 'yan Najeriya 800 da aka kora aiki saboda shn shiga kungiyar ta PENGASSAN. PENGASSAN ta dauki wannan mataki ne a ranar Lahadi bayan data fara yajin aikin sai abinda hali yayi.
Tabbas Goodluck Jonathan zai tsaya takarar shugaban kasa a 2027 a jam’iyyar PDP>>Farfesa Jerry Ghana

Tabbas Goodluck Jonathan zai tsaya takarar shugaban kasa a 2027 a jam’iyyar PDP>>Farfesa Jerry Ghana

Duk Labarai
Farfesa Jerry Ghana ya bayar da tabbacin cewa, tsohon shugaba kasa, Farfesa Jerry Ghana zai sake tsayawa takarar shugaban kasa a jam'iyyar PDP a zaben shekarar 2027 me zuwa. Hakan ya bayyana ne bayan da rade-radin fitowar tsohon shugaba kasar takara ke kara yaduwa. Farfesa Jerry Ghana yace tun bayan faduwar tsohon shugaban kasan zabe a shekarar 2015, an samu shugaban kasar da yayi shekara 8 yana mulki kuma gashi an sake samun wani yayi shekaru 2 amma har yanzu 'yan Najeriya ta kiran Goodluck Jonathan ya dawo. Yace PDP jam'iyya ce ta Adalci da ke baiwa 'yan Najeriya abinda suka zaba.
Kalli Bidiyon: Muna muna kan Kalaman Sheikh Lawal Triumph kuma nasan cewa, a cikin Mintuna 10 zai kawo hujjojin kalaman da yayi>>Inji Sheikh Sani Rijiyar Lemu

Kalli Bidiyon: Muna muna kan Kalaman Sheikh Lawal Triumph kuma nasan cewa, a cikin Mintuna 10 zai kawo hujjojin kalaman da yayi>>Inji Sheikh Sani Rijiyar Lemu

Duk Labarai
Malamin Addinin Islama, Sheikh Sani Rijiyar Lemu ya bayyana goyon baya ga Malam Lawal Triumph game da zargin da ake masa na yiwa Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) Batanci. Sheikh Sani yace Kalaman da malam yayi suna tare dashi suma akan irin wannan fatawar suke. Yace da ake cewa wai idan ba'a kama Lawal Triumph ba, shima Abduljabbar a sakeshi, yace idan so suke a saki Abduljabbar su fito kawai su fada ba sai sun yiwa wani sharri ba. https://www.tiktok.com/@tijjanihassangwale/video/7554523563399580946?_t=ZS-906OnuDGFDV&_r=1