A yayin da yake sukar Gwamnatin Muslim Muslim, an gano cewa Rev. Ezekiel Dachomo na daga cikin wadanda matar shugaban kasa, Remi Tinubu ta rabawa kudade a jihar Filato
A wata hira da Channels TV suka yi dashi, Rev. Ezekiel Dachomo ya bayyana cewa, mulkin Muslim Muslim shine babbar cin zarafi da akawa Kiristoci a Najeriya.
Saidai wasu sun zakulo sunansa a cikin wadanda auka amfana da tallafin kudaden da matar shugaban kasa, Remi Tinubu ta bayar a jihar Filato.
Da yawa dai sun bayyana cewa, bai kamata yana zagin wannan gwamnati ba musamman lura da cewa ya amfana da ita.
https://twitter.com/Abdul_Ahmad_/status/1995582978378920442?t=PdCuIx6oWE2tK18QRy6a4Q&s=19








