Abin takaici, Kasar China ce kadai cikin kasashen Duniya ta nuna da gaske tana tare da Najeriya tun bayan Bharazanar Amurka
Rahotanni sun nuna cewa, kasar China ce kadai ta nuna da gaske take tana tare da Najeriya bayan barazanar da kasar Amurka ta yi na shigowa Najeriya dan yakar wadanda ta kira da cewa sunawa Kiristoci Khisan Kyiyashi.
Kasar China ta nuna tana tare da Najeriya ne saboda tana da karfin dangantaka ta tattalin Arziki a Najeriya kuma Amurka zata zo ne dan ta lalata wannan dangantakar.
Abin mamaki shine ko kasar Ingila da ta reni Najeriya bata nuna goyon baya ga Najeriya ba.
Saidai kungiyar hadin kan kasashen Turai EU ta nuna cewa a girmama kasancewar Najeriya a matsayin kasa me zaman kanta, wanda hakan na jeka nayi kane.
Kasar Saudiyya da sauran kasashen Larabawa wadanda su ma suna da dangantaka me karfi da kasar Amurka sun kasa fitowa su nuna suna tare da Najeriya duk da yawan musul...








