Sule Lamido Yayi Barzanar kai PDP kotu saboda an ki sayar masa da Fom din tsayawa takarar shugaban jam’iyyar
Tsohon Gwamnan Jigawa, Sule Lamido yayi barzanar Kai jami'iyyarsa ta PDP kara kotu.
Sule Lamido ya bayyana hakane bayan kasa sayen Fom din tsayawa takarar shugaban jam'iyyar a ranar Litinin
Yace idan bai samu damar sayar fom din ba zai iya garzayawa kotu dan jin dalilin da yasa aka hanashi.
A baya dai, Sule Lamido ya bayyana aniyarsa ta son tsayawa takarar shugaban jam'iyyar PDP a shafinsa na Facebook.
Saidai wasu manya a jam'iyyar sun bayyana cewa, Kabiru Tanimu Turaki suke son tsayarwa a matsayin shugaban jam'iyyar








