Malam Rigi-Rigi ya bada lakani ga wadanda ke yawan haihuwa amma 'ya'yansu basa rayuwa suna yawan mutuwa.
Yace a sakawa yaron sunan Yahya zai.
https://www.tiktok.com/@hafizuuba/video/7534666630597446968?_t=ZS-8ye32DktnaC&_r=1
Babban Malamin Addinin Islama, Sheikh Abdallah Gadon kaya yayi kiran shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya karrama yara mata da suka yi nasarar lashe gasar Turanci ta Duniya tare da iyayensu.
Yace ya kamata a karrama hadda iyayensu saboda yanda suka kula dasu suka basu tarbiyya da ilimi da har suka kai wannan mataki.
Malam yace ba 'yan kwallo kadai shugaban kasar zai rika karramawa ba.
inda yace shugaban zai bar mummunan tarihi idan bai karrama wadannan yara ba.
https://www.tiktok.com/@abdul_prince_/video/7535249986481622328?_t=ZS-8ye0ppEjQ37&_r=1
Wannan kira na malam na zuwane bayan na Sheikh Isa Ali Pantami na cewa ya kamata shugaba Tinubu yawa yaran irin karramawar da yawa 'yan Kwallon Najeriya.
Wannan matashin ya shiga mamaki bayan da wata ta masa comment da cewa wai tana son yayi lalata da ita ko da sau daya ne.
https://www.tiktok.com/@user.beelarl/video/7535122952174554424?_t=ZS-8ydz24HSNfN&_r=1
Wasu dai na cewa, Ba lallai macece ta masa magana ba, watakila namijine.
Tauraruwar Tiktok, Nafisa Ishak ta bayyana damuwa game da yanda wasu maza ke wa matan da suka aura rikon sakainar kashi.
Ta bayar da misali da kanta cewa tana gidan miji duk ta lalace amma data fito sai da ta ci sama da Tiriliyan 3 kamin ta zama yanda ake kallonta.
Ta yi kira ga maza da su ji tsoron Allah akan yanda suke rikon mata.
Wadannan kalamai nata sun jawo cece-kuce sosai.
https://www.tiktok.com/@nafisa_ishak/video/7533924472827415864?_t=ZS-8ydvIyOE6l6&_r=1
Dan majalisar tarayya daga Zamfara Kabiru Mai Palace ya gayara makabartu 80 a jihar.
Da yake magana da manema labarai ranar Talata wajan kaddamar da aikin, yace kowane mutum idan ya rasu makabarta za'a kai a binneshi.
Makabartun da aka gyara na tsakanin kananan Hukumomin Tsafe da Gusau ne
Ya kuma bayyana cewa gyaran ya zama dole lura da halin lalacewa da makabartun suke.
Ya sha Alwashin daukar masu gadin makabartar da kuma biyansu Haraji.
Tauraruwar Fina-finan Hausa dake a Kaduna, Ummi Hutu ta yi korafin cewa, an daina sakata a fim saboda bata bada hadin kai.
Ta bayyana hakane a wani Bidiyon ta daya bayyana a Tiktok.
Tace Amma ta samu wata harkar shine ake mata bita da kulli ana mata bakin ciki amma tace masu yi basu isa ba.
https://www.tiktok.com/@iya_habu/video/7535086847328914694?_t=ZS-8ydKY609Agr&_r=1
Babban malamin Addinin Islama, Sheikh Salihu Zaria ya bayyana cewa yana da sha'awar zama sanata.
Yace ba zasu rika bari wadanda basu cancanta ba su ci gaba da mulkar mutane ba.
Yace zai fito takarar sanata kuma babu wanda ya isa yasa ya janye.
https://www.tiktok.com/@yunus.abu.bakr6/video/7534836390903745848?_t=ZS-8ydK7oiav8T&_r=1
Tauraruwar fina-finan Hausa, Ladidi tubeless ta bayyana cewa, ta taba aure a baya amma auren ya mutu.
Tace bata taba haihuwa ba amma tana fatan nan gaba ta sake yin aure ta haihu.
Ladidi Tubeless ta bayyana hakane a hirar da BBCHausa suka yi da ita.
https://www.tiktok.com/@ladidi_tubbles/video/7535082673556032824?_t=ZS-8ydI3fmSNjF&_r=1