Thursday, December 18
Shadow
Kalli Bidiyon: Ba yaran nan kadai, har iyayensu ya kamata Shugaba Tinubu ya karramasu>>Inji Sheikh Gadon Kaya

Kalli Bidiyon: Ba yaran nan kadai, har iyayensu ya kamata Shugaba Tinubu ya karramasu>>Inji Sheikh Gadon Kaya

Duk Labarai
Babban Malamin Addinin Islama, Sheikh Abdallah Gadon kaya yayi kiran shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya karrama yara mata da suka yi nasarar lashe gasar Turanci ta Duniya tare da iyayensu. Yace ya kamata a karrama hadda iyayensu saboda yanda suka kula dasu suka basu tarbiyya da ilimi da har suka kai wannan mataki. Malam yace ba 'yan kwallo kadai shugaban kasar zai rika karramawa ba. inda yace shugaban zai bar mummunan tarihi idan bai karrama wadannan yara ba. https://www.tiktok.com/@abdul_prince_/video/7535249986481622328?_t=ZS-8ye0ppEjQ37&_r=1 Wannan kira na malam na zuwane bayan na Sheikh Isa Ali Pantami na cewa ya kamata shugaba Tinubu yawa yaran irin karramawar da yawa 'yan Kwallon Najeriya.
Da Duminsa: Gwamnati ta fitar da gargadin Ambaliyar ruwan da za’a kwashe kwanaki 5 ana yi a jihohi 19, karanta jadawalin Jihohin

Da Duminsa: Gwamnati ta fitar da gargadin Ambaliyar ruwan da za’a kwashe kwanaki 5 ana yi a jihohi 19, karanta jadawalin Jihohin

Duk Labarai
Gwamnati tacw za'a kwashe kwanaki 5 ana ruwan sama a jere wanda hakan zai iya jawo ambaliyar ruwa a jihohi 19 da furare 76. Bangaren kula da ambaliyar ruwa na ma'aikatar Muhalli ne ya fitar da wannan sanarwar. Hakan na zuwane yayin da ambaliyar ruwan tuni ta shiga jihohin Gombe, Plateau, Ogun, Anambra, Delta, da Legas a ranar Talata. Wannan ambaliyar ruwa a cewar sanarwar zata fara ne daga ranar 5 zuwa 9 ga watan Augusta. Garuruwan da lamarin zai shafa sun hada da Akwa-Ibom (Edor, Eket, Ikom, Oron, Upenekang); Bauchi (Tafawa-Balewa, Azare, Jama’are, Kari, Misau, Jama’a); Ebonyi (Abakaliki, Echara, Ezilo); Cross-River (Ogoja Edor, Obubra); Nasarawa (Keana, Keffi, Wamba); Benue (Agaku, Buruku, Gboko, Igumale, Ito, Katsina-Ala, Ugba, Vande-Ikya); Kaduna (Jaji, Kafancha, Birnin-Gwa...
A wane littafin aka ce sai an sha wuya a gidan aure? Maza ku ji tsoron Allah sai ku auri mace tubarkallah amma bayan wata 7 ta rame ta lalace>> Inji Nafisa Ishak

A wane littafin aka ce sai an sha wuya a gidan aure? Maza ku ji tsoron Allah sai ku auri mace tubarkallah amma bayan wata 7 ta rame ta lalace>> Inji Nafisa Ishak

Duk Labarai
Tauraruwar Tiktok, Nafisa Ishak ta bayyana damuwa game da yanda wasu maza ke wa matan da suka aura rikon sakainar kashi. Ta bayar da misali da kanta cewa tana gidan miji duk ta lalace amma data fito sai da ta ci sama da Tiriliyan 3 kamin ta zama yanda ake kallonta. Ta yi kira ga maza da su ji tsoron Allah akan yanda suke rikon mata. Wadannan kalamai nata sun jawo cece-kuce sosai. https://www.tiktok.com/@nafisa_ishak/video/7533924472827415864?_t=ZS-8ydvIyOE6l6&_r=1
Dan majalisar tarayya daga jihar Zamfara Kabiru Mai Palace ya gyara makabartu 80 a matsayin aikin da yawa mazabarsa

Dan majalisar tarayya daga jihar Zamfara Kabiru Mai Palace ya gyara makabartu 80 a matsayin aikin da yawa mazabarsa

Duk Labarai
Dan majalisar tarayya daga Zamfara Kabiru Mai Palace ya gayara makabartu 80 a jihar. Da yake magana da manema labarai ranar Talata wajan kaddamar da aikin, yace kowane mutum idan ya rasu makabarta za'a kai a binneshi. Makabartun da aka gyara na tsakanin kananan Hukumomin Tsafe da Gusau ne Ya kuma bayyana cewa gyaran ya zama dole lura da halin lalacewa da makabartun suke. Ya sha Alwashin daukar masu gadin makabartar da kuma biyansu Haraji.
Kalli Bidiyo: Yanda aka daina sakani a Fim saboda bana bada hadin kai ayi…. dani>>Inji jarumar fina-finan Hausa, Ummi Hutu

Kalli Bidiyo: Yanda aka daina sakani a Fim saboda bana bada hadin kai ayi…. dani>>Inji jarumar fina-finan Hausa, Ummi Hutu

Duk Labarai
Tauraruwar Fina-finan Hausa dake a Kaduna, Ummi Hutu ta yi korafin cewa, an daina sakata a fim saboda bata bada hadin kai. Ta bayyana hakane a wani Bidiyon ta daya bayyana a Tiktok. Tace Amma ta samu wata harkar shine ake mata bita da kulli ana mata bakin ciki amma tace masu yi basu isa ba. https://www.tiktok.com/@iya_habu/video/7535086847328914694?_t=ZS-8ydKY609Agr&_r=1
Kalli Bidiyo: Babban Burina shine in zama Sanata, Zan Fito takara kuma babu wanda ya isa yasa in janye>>Inji Sheikh Salihu Zaria

Kalli Bidiyo: Babban Burina shine in zama Sanata, Zan Fito takara kuma babu wanda ya isa yasa in janye>>Inji Sheikh Salihu Zaria

Duk Labarai
Babban malamin Addinin Islama, Sheikh Salihu Zaria ya bayyana cewa yana da sha'awar zama sanata. Yace ba zasu rika bari wadanda basu cancanta ba su ci gaba da mulkar mutane ba. Yace zai fito takarar sanata kuma babu wanda ya isa yasa ya janye. https://www.tiktok.com/@yunus.abu.bakr6/video/7534836390903745848?_t=ZS-8ydK7oiav8T&_r=1
Kalli Bidiyon: Na taba aure sau daya amma yanzu bani da aure amma ina fatan in yi aure in haihu>>Inji Ladidi

Kalli Bidiyon: Na taba aure sau daya amma yanzu bani da aure amma ina fatan in yi aure in haihu>>Inji Ladidi

Duk Labarai
Tauraruwar fina-finan Hausa, Ladidi tubeless ta bayyana cewa, ta taba aure a baya amma auren ya mutu. Tace bata taba haihuwa ba amma tana fatan nan gaba ta sake yin aure ta haihu. Ladidi Tubeless ta bayyana hakane a hirar da BBCHausa suka yi da ita. https://www.tiktok.com/@ladidi_tubbles/video/7535082673556032824?_t=ZS-8ydI3fmSNjF&_r=1