Monday, March 2
Shadow
Kalli Bidiyo: Wallahi Dan Damusa bai Rasu yana aikata abinda kuke zaagiynsa akai ba>>Inji Me_Rayyan

Kalli Bidiyo: Wallahi Dan Damusa bai Rasu yana aikata abinda kuke zaagiynsa akai ba>>Inji Me_Rayyan

Duk Labarai
Me_Rayyan ya bayyana cewa, Wallahi Dan Damusa bai mutu yana aikata abonda ake zarginsa da aikatawa ba. Yace a lokacin da aka yi sulhu da dan Damusa a Masallaci a Kaduna sun halarci wajan, yace wadanda basu yadda ayi Sulhu ba, Dan Damusa da jami'an tsaro ake zuwa ace su yadda ayi sulhun. https://www.tiktok.com/@me_rayyana/video/7547474386085793031?_t=ZS-8zjxZOdn2iv&_r=1 Rasuwar Dan Damusa dai ta tayar da kura sosai musamman a kafafen sadarwa inda akai ta maganganu da muhawara kala-kala.
Karfin Hali kawai nike ina yin Fim, Yanzu haka ana neman Miliyan 2 dan yimin aikin ciwon zuciya>>Inji Tahir Fage

Karfin Hali kawai nike ina yin Fim, Yanzu haka ana neman Miliyan 2 dan yimin aikin ciwon zuciya>>Inji Tahir Fage

Duk Labarai
Tauraron fina-finan Hausa, Tahir Fage ya bayyana cewa, karfin hali yake fina-finan da yake fitowa saboda yana fama da ciwon zuciya Yace ana neman sama da Naira Miliyan 2 dan a masa aiki a Abuja. Ya bayyana hakane a hirar da RFIHausa Suka yi dashi. Ya kuma ce Ko rawar gala da aka ga yayi a kwanakin baya yana neman dubu 250 ne yaran da suka bude gidan galar suka bashi Naira dubu 100 dan ya je a matsayin babban bako. https://www.tiktok.com/@rfi_ha/video/7549833237225278737?_t=ZS-8zjQtmXQvCr&_r=1
Daga yanzu sai limamai sun rika gabatar da Hudubar Juma’a an tantance bata sabawa tsarin Gwamnati ba kamin a amince su hau Munbari su yi ta>>Inji Gwamnan jihar Naija, Umar Bago

Daga yanzu sai limamai sun rika gabatar da Hudubar Juma’a an tantance bata sabawa tsarin Gwamnati ba kamin a amince su hau Munbari su yi ta>>Inji Gwamnan jihar Naija, Umar Bago

Duk Labarai
Gwamnan jihar Naija, Umar Bago ya bayyana cewa, daga yanzu sai an tantance hudubar Juma'a kamin a yadda limami ya hau Mumbari ya gabatar da ita. Gwamnan ya tabbatar da hakan ne a hirar da aka yi dashi a hidan Talabijin na TVC ranar Lahadi. Yace ba zasu amince da a rika yada hudubar data zama zata cutar da mutane ko gwamnati ba. Gwamnan ya kara da cewa, suna aiki da hukumomin tsaro dan tabbatar da faruwar hakan.
Likitoci a Najeriya sun janye yajin aikin gargaɗi

Likitoci a Najeriya sun janye yajin aikin gargaɗi

Duk Labarai
Ƙungiyar likitoci masu neman ƙwarewa a Najeriya ta janye yajin aikin gargaɗi da ta fara ranar Juma'a sakamakon ƙorafe-ƙorafen da suka shafi rashin kulawa daga ɓangaren gwamnati. Wata sanarwa da ƙungiyar Nigerian Association of Resident Doctors (Nard) ta fitar ta ce ta janye yajin aikin na kwana biyar ne bayan gwamnatin Najeriya ta amince da fara biyan wasu buƙatunsu. "Bayan yunƙurin da gwamnati ta nuna na biyan wasu buƙatun da muka sanar, da kuma shirin fara biyan alawus ga ma'aikatan da ke bin bashi...mun amince mu janye yajin aikin daga ƙarfe 8:00 na safiyar Lahadi," in ji sanarwar. Ta ƙara da cewa ta bai wa gwamnatin tarayyar wa'adin mako biyu domin aiwatar da alƙawuran da ta ɗauka.
Duk me cewa, bamu zaman Aure, yawa kansa Arziki>>Inji Tauraruwar fina-finan Hausa, Kilishi

Duk me cewa, bamu zaman Aure, yawa kansa Arziki>>Inji Tauraruwar fina-finan Hausa, Kilishi

Duk Labarai
Tauraruwar fina-finan Hausa, Kilishi ta bayyana rashin jin dadinta kan kalaman da ake yi musamman akan taurarin fina-finan mata da cewa basa son zaman aure. Ta bayyana hakane a wani Bidiyon ta dake yawo a kafafen sadarwa inda tace Aure mutuwa da haihuwa duk na Allah ne. Tace wanda kuma bai yadda ba sai yawa kansa Arziki. https://www.tiktok.com/@tuna__baya/video/7549901451414359351?_t=ZS-8zjGoTxkZQ9&_r=1
Matasa indai kun shirya da gaske kuke, wallahi cikin sauki zaku kwace mulki daga hannun tsofaffinnan da suka hana kasarnan ci gaba>>Inji Sarkin Kano, Muhammad Sanusi II

Matasa indai kun shirya da gaske kuke, wallahi cikin sauki zaku kwace mulki daga hannun tsofaffinnan da suka hana kasarnan ci gaba>>Inji Sarkin Kano, Muhammad Sanusi II

Duk Labarai
Me martaba Sarkin Kano, Muhammad Sanusi II ya bayyanawa matasa cewa cikin sauki zasu karbe mulki a kasarnan indai suka ce abinda ake musu ya isa haka. Ya bayyana hakane a wajan wani taron marubuta da aka yi, kamar yanda gidan talabijin na Channels TV ya ruwaito. Sarki Sanusi yace Najeriya ta yi fama da rashin shuwagabanni na gari wanda hakan ya hanata samun ci gaban da ya kamata.
Nima bana neman taimakon Inyas ko taimakon Manzon Allah(SAW), Taimakon Allah kawai nake nema>>Inji Malam Abdulrahman Umar

Nima bana neman taimakon Inyas ko taimakon Manzon Allah(SAW), Taimakon Allah kawai nake nema>>Inji Malam Abdulrahman Umar

Duk Labarai
Malam Abdulrahman Umar ya bayyana cewa, baya neman taimakon Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) ko taimakon Inyass. Yace Taimakon Allah kawai yake nema. Malam ya bayyana hakane a wajan wa'azinsa. https://www.tiktok.com/@isah_bello_assalafy_garo/video/7549655866891422997?_t=ZS-8ziWMkt2bce&_r=1 Marigayi, Dr. Idris Dutsen Tanshi ne ya fara yin wadannan kalamai a baya wadanda suka jawo cece-kuce sosai.
Dangote na sayarwa da kasashen waje mai a farashi me sauki fiye da Najeriya>>’Yan kasuwar mai suka koka

Dangote na sayarwa da kasashen waje mai a farashi me sauki fiye da Najeriya>>’Yan kasuwar mai suka koka

Duk Labarai
'Yan kasuwar man fetur sun koka da cewa, Dangote na sayarwa da kasashen waje man fetur a farashi me sauki fiye ye da yanda yake sayarwa a Najeriya. ''Yan kasuwar sun ce 'yan kasar waje na samun ragin kusan Naira 65 akan kowace Lita idan aka kwatanta da farashin man da Dangoten ke sayarwa a Najeriya. Dan hakane ma suka ce wani lokacin basa saye a wajan Dangote sai su je wajan 'yan kasar wajen da ya sayarwa su saya a hannunsu su shigo dashi Najeriya. Shugaban kungiyar 'yan kasuwar DAPPMAN, Olufemi Adewole ne ya bayyana haka ga manema labarai na Punchng. Yace abinda suke nema a wajan Dangote shine ya rika musu sauki dan haka sai su daina shigo da man daga kasashen waje suna saye a hannunshi. Yace Dangote da gangan yake karya farashin mai da zarar ya ga sun kawo mai daga gasa...
Labarin cewa tsohuwar matar Ahmad XM, Safiya zata auri Hambali ba gaskiya bane

Labarin cewa tsohuwar matar Ahmad XM, Safiya zata auri Hambali ba gaskiya bane

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Labarin dake yawo cewa, tsohuwar matar Ahmad XM, Watau Safiya zata auri Hambali ba gaskiya bane. Safiyar da kanta ta fito ta musanta wannan labari inda kuma wasu na kusa da ita suma duk suka karyata wannan labari. Bayan rabuwarta da tsohon mijinta, Ahmad XM, An yada labaran cewa zata sake aure inda zata auri Hambali, kuma da dama sun zata hakan gaskiyane. Saidai daga baya labari ya bayyana cewa, ba gaskiya bane wannan ikirarin.